< Ishaya 34 >
1 Ku zo kusa, ku al’ummai, ku kuwa saurara ku kasa kunne, ku mutane! Bari duniya ta ji, da kuma dukan abin da yake cikinta, duniya, da dukan abin da yake fitowa daga gare ta!
Pridite bliže, vi narodi, da slišite in prisluhnite ve ljudstva. Naj zemlja sliši in vsi, ki so na njej, zemeljski [krog] in vse stvari, ki pridejo iz njega.
2 Ubangiji yana fushi da dukan al’ummai; hasalarsa tana a kan mayaƙansu. Zai hallaka su tas, zai ba da su a karkashe.
Kajti ogorčenje od Gospoda je nad vsemi narodi in njegova razjarjenost nad vsemi njihovimi vojskami. Popolnoma jih je uničil, izročil jih je v klanje.
3 Za a jefar da waɗanda aka kashe gawawwakinsu za su yi wari; duwatsu za su jiƙu da jininsu.
Tudi njihovi umorjeni bodo vrženi ven in njihov smrad bo prišel iz njihovih trupel in gore bodo stopljene z njihovo krvjo.
4 Za a tumɓuke dukan taurarin sammai za a kuma nannaɗe sararin sama kamar littafi; dukan rundunar sama za su fāffāɗi kamar ganyayen da suka yanƙwane daga kuringa, kamar’ya’yan ɓauren da suka bushe daga itacen ɓaure.
Vse vojske neba bodo razpadle in nebo bo zvito skupaj kakor zvitek pergamenta. Vse njihove vojske bodo padle, kakor list pade s trte in kakor figa pade iz figovega drevesa.
5 Takobina ya sha zararsa a cikin sammai; duba, ya sauko cikin hukunci a kan Edom, mutanen da zan hallaka tas.
Kajti moj meč bo potešen na nebu. Glejte, ta bo prišel dol nad Edóm in nad ljudstvo mojega prekletstva, k sodbi.
6 Takobin Ubangiji ya jiƙu da jini, ya rufu da kitse, jinin raguna da na awaki, kitse daga ƙodar raguna. Gama Ubangiji ya yi hadayar Bozra da kuma babban kisa a Edom.
Gospodov meč je poln krvi, zamaščen s tolščo in s krvjo jagnjet in koz, s tolščo ledvic ovnov, kajti Gospod ima klavno daritev v Bocri in velik pokol v edómski deželi.
7 Babban bijimin jeji zai fāɗi tare da su, maruƙan bijimi da manyan bijimai. Ƙasarsu za tă cika da jini, ƙura kuma zai cika da kitse.
Samorogi bodo z njimi prišli dol in bikci z biki in njihova dežela bo namočena s krvjo in njihov prah zamaščen z mastnostjo.
8 Gama Ubangiji yana da ranar ɗaukar fansa, shekarar ramuwa, don biya wa Sihiyona bukata.
Kajti to je dan Gospodovega maščevanja in leto povračil zaradi Sionove pravde.
9 Za a mai da rafuffukan Edom rami, ƙurarta za tă zama kibiritun farar wuta; ƙasarta za tă zama rami mai ƙuna!
Njegovi vodotoki bodo spremenjeni v smolo, njegov prah v žveplo in njegova dežela bo postala goreča smola.
10 Ba za a kashe ta ba dare da rana; hayaƙinta za tă yi ta tashi har abada. Daga tsara zuwa tsara za tă zama kango; babu wani da zai ƙara wucewa ta wurin.
Ta ne bo pogašena ne ponoči ne podnevi; njen dim se bo dvigoval na veke. Od roda do roda bo ležala opustošena; nihče ne bo šel skoznjo na veke vekov.
11 Mujiyar hamada da mujiya mai kuka za su mallake ta; babban mujiya da hankaka za su yi sheƙa a can. Allah zai miƙe a kan Edom magwajin bala’i da ma’aunin kango.
Toda kormoran in bobnarica jo bosta vzela v last; tudi sova in krokar bosta v njej prebivala. Nadnjo bo razširil vrvico zmede in kamne praznine.
12 Sarakunanta ba za su kasance da wani abin da ake kira masarauta ba, dukan sarakunanta za su ɓace.
Njene plemenite bodo poklicali h kraljestvu, toda tam ne bo nikogar in vsi njeni princi bodo nič.
13 Ƙayayuwa za su mamaye fadodinta ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya za su cika kagaranta. Za tă zama mazaunin diloli da gida don mujiyoyi.
Trnje bo pognalo v njenih palačah, koprive in trnovo grmovje v njenih trdnjavah, in ta bo prebivališče zmajem in dvor za sove.
14 Halittun hamada za su sadu da kuraye, awakin jeji za su yi ta kiran juna; a can halittun dare su ma za su huta su kuma nemi wurin hutu wa kansu.
Divje živali iz puščave se bodo prav tako srečale z divjimi živalmi z otoka in kozjenog bo klical svojemu tovarišu; tudi skovir bo tam počival in zase našel mesto počitka.
15 Mujiya za tă yi sheƙa a can ta zuba ƙwai; za tă ƙyanƙyashe su, ta kuma kula da’ya’yanta a inuwar fikafikanta; a can kuma shirwa za su taru, kowa da abokinsa.
Tam si bo velika sova naredila svoje gnezdo, polegla, izvalila in [jih] zbrala pod svojo senco. Tam bodo zbrani tudi jastrebi, vsak s svojo družico.
16 Duba a cikin littafin Ubangiji ka kuma karanta. Babu wani a cikin waɗannan da ya ɓace, babu ko ɗaya da ba ta da abokiya. Gama bakinsa ne ya ba da umarni, Ruhunsa kuma zai tara su wuri ɗaya.
Poiščite si iz Gospodove knjige in berite. Nobeden izmed teh ne bo manjkal, nobeden ne bo pogrešal svoje družice, kajti moja usta so to zapovedala in njegov duh jih je zbral.
17 Ya ba su rabonsu; hannunsa ya rarraba musu ta wurin awo. Za su mallake ta har abada su kuma zauna a can daga tsara zuwa tsara.
Zanje je vrgel žreb in njegova roka jim je to razdelila po vrvici. Vzeli jo bodo v last na veke, od roda do roda bodo prebivali v njej.