< Ishaya 33 >

1 Kaitonka, ya kai mai hallakarwa, kai da ba a hallakar da kai ba! Kaitonka, ya maciya amana, kai da ba a ci amanarka ba! Sa’ad da ka daina hallakarwa, za a hallaka ka; sa’ad da ka daina cin amana, za a ci amanarka.
Gorje tebi, ki pleniš, pa nisi bil oplenjen in postopaš zahrbtno, oni pa niso zahrbtno postopali s teboj! Ko boš prenehal pleniti, potem boš oplenjen in ko boš naredil konec zahrbtnemu postopanju, potem bodo zahrbtno postopali s teboj.
2 Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai; muna marmarinka. Ka zama ƙarfinmu kowace safiya, cetonmu a lokacin damuwa.
Oh Gospod, bodi nam milostljiv, pričakovali smo te. Vsako jutro bodi njihov laket, tudi naša rešitev duše v času stiske.
3 Da tsawar muryarka, mutane za su gudu; sa’ad da ka tashi, al’ummai za su watse.
Ob hrupu upora je ljudstvo pobegnilo, ob tvojem vzdigovanju so bili narodi razkropljeni.
4 Ganimarku, ya al’ummai ƙanana fāri sun girbe; kamar tarin fārin da mutane sun fāɗa wa.
Vaš plen bo zbran kakor zbiranje gosenice, kakor tekanje leteče kobilice sem ter tja bo on tekel nad njimi.
5 Ubangiji da girma yake, gama yana zaune a bisa; zai cika Sihiyona cikin gaskiya da adalci.
Gospod je povišan, kajti prebiva na višavi. Sion je napolnil s sodbo in pravičnostjo.
6 Zai zama tabbataccen harsashi na koyaushe, ma’ajin ceto da hikima da sani a yalwace; tsoron Ubangiji shi ne mabuɗin wannan dukiya.
Modrost in spoznanje bosta stabilnost tvojih časov in moč rešitve duše. Gospodov strah je njegov zaklad.
7 Duba, jarumawansu suna kuka da ƙarfi a tituna; jakadun salama suna kuka mai zafi.
Glej, njihovi hrabri bodo zunaj vreščali. Predstavniki miru bodo grenko jokali.
8 An gudu an bar manyan hanyoyi, babu matafiye a kan hanyoyi. Aka keta yarjejjeniya, an rena shaidunsa ba a kuwa ganin girman kowa.
Glavne ceste ležijo zapuščene, popotnik peša. Prelomil je zavezo, preziral mesta, ne ozira se na nobenega človeka.
9 Ƙasa tana kuka an kuma gudu an bar ta, Lebanon ta sha kunya ta kuma yanƙwane; Sharon ta zama kamar Araba, Bashan da Karmel sun kakkaɓe ganyayensu.
Zemlja žaluje in peša. Libanon je osramočen in posekan. Šarón je podoben divjini in Bašán ter Karmel otresata svoje sadove.
10 “Yanzu zan tashi,” in ji Ubangiji. “Yanzu ne za a ɗaukaka ni; yanzu za a ɗaga ni sama.
»Sedaj bom vstal, « govori Gospod, »sedaj bom povišan, sedaj se bom dvignil.
11 Kun yi cikin yayi, kuka haifi kara; numfashinku wuta ne da zai cinye ku.
Spočeli boste pleve, rodili boste strnišče. Vaš dih vas bo pogoltnil kakor ogenj.
12 Za a ƙone mutane kamar da ƙuna farar ƙasa; kamar ƙayayyuwan da aka sare aka kuma sa musu wuta.”
Ljudstvo bo kakor gorenje žganega apna, kakor posekano trnje bodo sežgani v ognju.
13 Ku da kuke da nesa, ku ji abin da na yi; ku da kuke kusa, ku san ikona!
Prisluhnite vi, ki ste daleč proč, kaj sem storil in vi, ki ste blizu, priznajte mojo moč.
14 Masu zunubi a Sihiyona sun firgita; rawar jiki ya kama marasa sanin Allah suna cewa, “Wane ne a cikinmu zai iya zama da wuta mai ci? Wane ne a cikinmu zai iya zama da madawwamiyar ƙonewa?”
Grešniki na Sionu so prestrašeni, grozljivost je presenetila hinavce. Kdo izmed nas bo bival s požirajočim ognjem? Kdo izmed nas bo bival z večnimi gorenji?
15 Shi da yake tafiya cikin adalci yana kuma magana abin da yake daidai, wanda yake ƙin riba daga cuta yana kuma kiyaye hannunsa daga karɓan cin hanci, wanda yake hana kunnuwansa daga ƙulla kisa ya kuma rufe idanunsa a kan tunanin aikata mugunta,
Kdor hodi pravično in govori iskreno, kdor prezira dobiček zatiranj, ki otresa svoji roki pred tem, da bi držal podkupnine, ki si ušesa zatiska pred poslušanjem o krvi in zatiska svoje oči pred gledanjem zla;
16 shi ne mutumin da zai zauna a bisa, wanda mafakarsa za tă zama kagarar dutse. Za a tanada abincinsa, kuma ruwa ba zai kāsa masa ba.
ta bo prebival na višavi. Njegov prostor obrambe bodo skalna oporišča. Dan mu bo kruh, njegove vode bodo zanesljive.
17 Idanunku za su ga sarki a cikin kyansa ku kuma hangi ƙasar da take shimfiɗe can da nisa.
Tvoje oči bodo videle kralja v njegovi lepoti. Gledale bodo deželo, ki je zelo daleč proč.
18 Cikin tunaninku za ku yi tunani firgitar da ta faru tun dā kuna cewa, “Ina hafsan nan? Ina wannan wanda yake karɓar haraji? Ina hafsan da yake lura da hasumiyoyi?”
Tvoje srce bo premišljevalo strahoto. Kje je pisar? Kje je prejemnik? Kje je tisti, ki je štel stolpe?
19 Ba za ku ƙara ganin waɗannan mutane masu girman kai kuma ba, waɗannan mutane masu magana da harshen da ba ku fahimta ba.
Ne boš videl krutega ljudstva, ljudstva globljega govora, kakor ga lahko zaznaš, jecljajočega jezika, ki ga ne moreš razumeti.
20 Ku duba Sihiyona, birnin shagulgulanmu; idanunku za su ga Urushalima, mazauni mai lafiya, tentin da ba za a taɓa gusar ba; wanda ba a taɓa tumɓuke turakunsa ba, ko a tsinke igiyoyinta.
Poglej na Sion, mesto naših slovesnosti. Tvoje oči bodo videle Jeruzalem, tiho prebivališče, šotor, ki ne bo porušen; niti eden izmed njegovih klinov ne bo nikoli odstranjen niti nobena izmed njegovih vrvi pretrgana.
21 A can Ubangiji zai zama Mai Iko Duka namu. Zai zama kamar inda manyan koguna da rafuffuka suke. Matuƙan jirgin ruwa ba za su kai wurinsu ba, manyan jiragen ruwa ba za su yi zirga-zirga a kansu ba.
Toda tam nam bo veličasten Gospod kraj širokih rek in vodotokov, kamor ne bo plula galeja z vesli niti čedna ladja ne bo plula mimo.
22 Gama Ubangiji ne alƙalinmu, Ubangiji ne mai ba mu dokoki, Ubangiji ne sarkinmu; shi ne wanda zai cece mu.
Kajti Gospod je naš sodnik, Gospod je naš zakonodajalec, Gospod je naš kralj, on nas bo rešil.
23 Maɗaurinku sun kunce ƙarfafan itacen jirgin ba su da kāriya, fikafikan jirgin ba su buɗu ba. Ta haka za a raba yalwar ganima har ma guragu za su kwashe ganimar.
Tvoja ladijska oprema je odvezana; ne morejo dobro ojačati jambora, ne morejo razpeti jadra. Potem je plen velikega ukradenega blaga razdeljen; hromi pobira plen.
24 Ba wani mazauna a Sihiyona da zai ce, “Ina ciwo”; za a kuma gafarta zunuban waɗanda suke zama a can.
Prebivalec ne bo rekel: »Bolan sem.« Ljudstvu, ki tam prebiva, bo odpuščena njihova krivičnost.

< Ishaya 33 >