< Ishaya 33 >

1 Kaitonka, ya kai mai hallakarwa, kai da ba a hallakar da kai ba! Kaitonka, ya maciya amana, kai da ba a ci amanarka ba! Sa’ad da ka daina hallakarwa, za a hallaka ka; sa’ad da ka daina cin amana, za a ci amanarka.
Wo to thee, that robbest; whether and thou schalt not be robbid? and that dispisist, whether and thou schalt not be dispisid? Whanne thou hast endid robbyng, thou schalt be robbid; and whanne thou maad weri ceessist to dispise, thou schalt be dispisid.
2 Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai; muna marmarinka. Ka zama ƙarfinmu kowace safiya, cetonmu a lokacin damuwa.
Lord, haue thou merci on vs, for we abiden thee; be thou oure arm in the morewtid, and oure helthe in the tyme of tribulacioun.
3 Da tsawar muryarka, mutane za su gudu; sa’ad da ka tashi, al’ummai za su watse.
Puplis fledden fro the vois of the aungel; hethene men ben scaterid of thin enhaunsyng.
4 Ganimarku, ya al’ummai ƙanana fāri sun girbe; kamar tarin fārin da mutane sun fāɗa wa.
And youre spuylis schulen be gaderid togidere, as a bruke is gaderid togidere, as whanne dichis ben ful therof.
5 Ubangiji da girma yake, gama yana zaune a bisa; zai cika Sihiyona cikin gaskiya da adalci.
The Lord is magnefied, for he dwellide an hiy, he fillid Sion with doom and riytfulnesse.
6 Zai zama tabbataccen harsashi na koyaushe, ma’ajin ceto da hikima da sani a yalwace; tsoron Ubangiji shi ne mabuɗin wannan dukiya.
And feith schal be in thi tymes; the ritchessis of helthe is wisdom and kunnynge; the drede of the Lord, thilke is the tresour of hym.
7 Duba, jarumawansu suna kuka da ƙarfi a tituna; jakadun salama suna kuka mai zafi.
Lo! seeris withoutenforth schulen crye, aungels of pees schulen wepe bittirli.
8 An gudu an bar manyan hanyoyi, babu matafiye a kan hanyoyi. Aka keta yarjejjeniya, an rena shaidunsa ba a kuwa ganin girman kowa.
Weies ben distried, a goere bi the path ceesside; the couenaunt is maad voide, he castide doun citees, he arettide not men.
9 Ƙasa tana kuka an kuma gudu an bar ta, Lebanon ta sha kunya ta kuma yanƙwane; Sharon ta zama kamar Araba, Bashan da Karmel sun kakkaɓe ganyayensu.
The lond morenyde, and was sijk; the Liban was schent, and was foul; and Saron is maad as desert, and Basan is schakun, and Carmele.
10 “Yanzu zan tashi,” in ji Ubangiji. “Yanzu ne za a ɗaukaka ni; yanzu za a ɗaga ni sama.
Now Y schal ryse, seith the Lord, now I schal be enhaunsid, and now I schal be reisid vp.
11 Kun yi cikin yayi, kuka haifi kara; numfashinku wuta ne da zai cinye ku.
Ye schulen conseyue heete, ye schulen brynge forth stobil; youre spirit as fier schal deuoure you.
12 Za a ƙone mutane kamar da ƙuna farar ƙasa; kamar ƙayayyuwan da aka sare aka kuma sa musu wuta.”
And puplis schulen be as aischis of the brennyng; thornes gaderid togidere schulen be brent in fier.
13 Ku da kuke da nesa, ku ji abin da na yi; ku da kuke kusa, ku san ikona!
Ye that ben fer, here what thingis Y haue do; and, ye neiyboris, knowe my strengthe.
14 Masu zunubi a Sihiyona sun firgita; rawar jiki ya kama marasa sanin Allah suna cewa, “Wane ne a cikinmu zai iya zama da wuta mai ci? Wane ne a cikinmu zai iya zama da madawwamiyar ƙonewa?”
Synneris ben al to-brokun in Syon, tremblyng weldide ipocritis; who of you mai dwelle with fier deuowringe? who of you schal dwelle with euerlastinge brennyngis?
15 Shi da yake tafiya cikin adalci yana kuma magana abin da yake daidai, wanda yake ƙin riba daga cuta yana kuma kiyaye hannunsa daga karɓan cin hanci, wanda yake hana kunnuwansa daga ƙulla kisa ya kuma rufe idanunsa a kan tunanin aikata mugunta,
He that goith in riytfulnessis, and spekith treuthe; he that castith awei aueryce of fals calenge, and schakith awei his hondis fro al yifte; he that stoppith his eeris, that he heere not blood, and closith his iyen, that he se not yuel.
16 shi ne mutumin da zai zauna a bisa, wanda mafakarsa za tă zama kagarar dutse. Za a tanada abincinsa, kuma ruwa ba zai kāsa masa ba.
This man schal dwelle in hiy thingis, the strengthis of stoonys ben the hiynesse of hym; breed is youun to hym, hise watris ben feithful.
17 Idanunku za su ga sarki a cikin kyansa ku kuma hangi ƙasar da take shimfiɗe can da nisa.
Thei schulen se the kyng in his fairnesse; the iyen of hym schulen biholde the londe fro fer.
18 Cikin tunaninku za ku yi tunani firgitar da ta faru tun dā kuna cewa, “Ina hafsan nan? Ina wannan wanda yake karɓar haraji? Ina hafsan da yake lura da hasumiyoyi?”
Eliachym, thin herte schal bithenke drede; where is the lettrid man? Where is he that weieth the wordis of the lawe? where is the techere of litle children?
19 Ba za ku ƙara ganin waɗannan mutane masu girman kai kuma ba, waɗannan mutane masu magana da harshen da ba ku fahimta ba.
Thou schalt not se a puple vnwijs, a puple of hiy word, so that thou maist not vndurstonde the fair speking of his tunge, in which puple is no wisdom.
20 Ku duba Sihiyona, birnin shagulgulanmu; idanunku za su ga Urushalima, mazauni mai lafiya, tentin da ba za a taɓa gusar ba; wanda ba a taɓa tumɓuke turakunsa ba, ko a tsinke igiyoyinta.
Biholde thou Sion, the citee of youre solempnyte; thin iyen schulen se Jerusalem, a riche citee, a tabernacle that mai not be borun ouer, nether the nailis therof schulen be takun awei withouten ende; and alle the cordis therof schulen not be brokun.
21 A can Ubangiji zai zama Mai Iko Duka namu. Zai zama kamar inda manyan koguna da rafuffuka suke. Matuƙan jirgin ruwa ba za su kai wurinsu ba, manyan jiragen ruwa ba za su yi zirga-zirga a kansu ba.
For oneli the worschipful doere oure Lord God is there; the place of floodis is strondis ful large and opyn; the schip of roweris schal not entre bi it, nethir a greet schip schal passe ouer it.
22 Gama Ubangiji ne alƙalinmu, Ubangiji ne mai ba mu dokoki, Ubangiji ne sarkinmu; shi ne wanda zai cece mu.
For whi the Lord is oure iuge, the Lord is oure lawe yyuere, the Lord is oure kyng; he schal saue vs.
23 Maɗaurinku sun kunce ƙarfafan itacen jirgin ba su da kāriya, fikafikan jirgin ba su buɗu ba. Ta haka za a raba yalwar ganima har ma guragu za su kwashe ganimar.
Thi roopis ben slakid, but tho schulen not auaile; thi mast schal be so, that thou mow not alarge a signe. Thanne the spuylis of many preyes schulen be departid, crokid men schulen rauysche raueyn.
24 Ba wani mazauna a Sihiyona da zai ce, “Ina ciwo”; za a kuma gafarta zunuban waɗanda suke zama a can.
And a neiybore schal seie, Y was not sijk; the puple that dwellith in that Jerusalem, wickidnesse schal be takun awei fro it.

< Ishaya 33 >