< Ishaya 33 >
1 Kaitonka, ya kai mai hallakarwa, kai da ba a hallakar da kai ba! Kaitonka, ya maciya amana, kai da ba a ci amanarka ba! Sa’ad da ka daina hallakarwa, za a hallaka ka; sa’ad da ka daina cin amana, za a ci amanarka.
Alas! thou plunderer when, thou, hadst not been plundered, And thou traitor when they had not betrayed thee: When thou hast ceased plundering, thou shalt be plundered, When thou hast left off betraying, they shall betray thee.
2 Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai; muna marmarinka. Ka zama ƙarfinmu kowace safiya, cetonmu a lokacin damuwa.
O Yahweh! shew us favour, —For thee, have we waited, —Be thou their arm every morning, Yea our salvation in the time of distress.
3 Da tsawar muryarka, mutane za su gudu; sa’ad da ka tashi, al’ummai za su watse.
At the noise of a tumult, the peoples retreated, —When thou didst lift thyself up, nations were scattered.
4 Ganimarku, ya al’ummai ƙanana fāri sun girbe; kamar tarin fārin da mutane sun fāɗa wa.
Then shall your spoil be gathered as the gathering of the caterpillar, —As the swift running of locusts, is he about to run upon them.
5 Ubangiji da girma yake, gama yana zaune a bisa; zai cika Sihiyona cikin gaskiya da adalci.
Exalted is Yahweh, for he inhabiteth a height, —He hath filled Zion with justice and righteousness.
6 Zai zama tabbataccen harsashi na koyaushe, ma’ajin ceto da hikima da sani a yalwace; tsoron Ubangiji shi ne mabuɗin wannan dukiya.
So shall a wealth of deliverances, wisdom and knowledge, become the stability of thy times, —the reverence of Yahweh, the same is his treasure.
7 Duba, jarumawansu suna kuka da ƙarfi a tituna; jakadun salama suna kuka mai zafi.
Lo! their heroes, have cried out openly, —the messengers of peace, in bitterness, continue weeping [they say]:
8 An gudu an bar manyan hanyoyi, babu matafiye a kan hanyoyi. Aka keta yarjejjeniya, an rena shaidunsa ba a kuwa ganin girman kowa.
The highways are deserted, The passer-by on the path, hath ceased, —He hath broken covenant, He hath despised cities, He hath made no account of men.
9 Ƙasa tana kuka an kuma gudu an bar ta, Lebanon ta sha kunya ta kuma yanƙwane; Sharon ta zama kamar Araba, Bashan da Karmel sun kakkaɓe ganyayensu.
The land mourneth, languisheth, Lebanon, displayeth shame, is withered, —Sharon, hath become, as the waste plain, And Bashan and Carmel are shaking off their leaves.
10 “Yanzu zan tashi,” in ji Ubangiji. “Yanzu ne za a ɗaukaka ni; yanzu za a ɗaga ni sama.
Now, will I arise, Saith Yahweh, Now, will I lift myself up, Now, will I be exalted!
11 Kun yi cikin yayi, kuka haifi kara; numfashinku wuta ne da zai cinye ku.
Ye shall conceive chaff Ye shall bring forth stubble, —Your own breath, like fire, shall devour you.
12 Za a ƙone mutane kamar da ƙuna farar ƙasa; kamar ƙayayyuwan da aka sare aka kuma sa musu wuta.”
So shall peoples, become, as the burnings of lime, —As thorns lopped off, with fire, shall they be burned.
13 Ku da kuke da nesa, ku ji abin da na yi; ku da kuke kusa, ku san ikona!
Hear—ye that are far off. what I have done, And know—ye that are near my might:
14 Masu zunubi a Sihiyona sun firgita; rawar jiki ya kama marasa sanin Allah suna cewa, “Wane ne a cikinmu zai iya zama da wuta mai ci? Wane ne a cikinmu zai iya zama da madawwamiyar ƙonewa?”
Terror-stricken in Zion, —are sinners, Shuddering hath seized the impious, —Who among us can sojourn with a fire that devoureth? Who among us can sojourn with burnings age-abiding?
15 Shi da yake tafiya cikin adalci yana kuma magana abin da yake daidai, wanda yake ƙin riba daga cuta yana kuma kiyaye hannunsa daga karɓan cin hanci, wanda yake hana kunnuwansa daga ƙulla kisa ya kuma rufe idanunsa a kan tunanin aikata mugunta,
He that walketh righteously, And speaketh uprightly, —He that refuseth the gain of exactions That shaketh his hands free from holding a bribe, That stoppeth his ear from hearkening to deeds of blood, And shutteth his eyes from giving countenance to wrong,
16 shi ne mutumin da zai zauna a bisa, wanda mafakarsa za tă zama kagarar dutse. Za a tanada abincinsa, kuma ruwa ba zai kāsa masa ba.
He, the heights, shall inhabit, A stronghold of crags, shall be his refuge, —His bread, hath been delivered, His waters, have been made sure,
17 Idanunku za su ga sarki a cikin kyansa ku kuma hangi ƙasar da take shimfiɗe can da nisa.
Of a king, in his beauty, shall thine eyes have vision: They shall see a land that stretcheth afar.
18 Cikin tunaninku za ku yi tunani firgitar da ta faru tun dā kuna cewa, “Ina hafsan nan? Ina wannan wanda yake karɓar haraji? Ina hafsan da yake lura da hasumiyoyi?”
Thy heart, may murmur in terror, —Where is the scribe? Where—the receiver? Where—he that maketh a list of the towers?
19 Ba za ku ƙara ganin waɗannan mutane masu girman kai kuma ba, waɗannan mutane masu magana da harshen da ba ku fahimta ba.
The fierce people, shalt thou not see, —The people of too deep a lip to be understood, of too barbarous a tongue for thee to comprehend.
20 Ku duba Sihiyona, birnin shagulgulanmu; idanunku za su ga Urushalima, mazauni mai lafiya, tentin da ba za a taɓa gusar ba; wanda ba a taɓa tumɓuke turakunsa ba, ko a tsinke igiyoyinta.
Look thou on Zion, the city of our appointed feast, —Thine own eyes, shall see Jerusalem—A home of comfort A tent which shall not be packed up—Whose pins shall not be pulled out, for ever, And none of, whose cords, shall be broken.
21 A can Ubangiji zai zama Mai Iko Duka namu. Zai zama kamar inda manyan koguna da rafuffuka suke. Matuƙan jirgin ruwa ba za su kai wurinsu ba, manyan jiragen ruwa ba za su yi zirga-zirga a kansu ba.
But, there shall Yahweh be our majestic one, A place of rivers—streams broad on both hands, Wherein shall go no galley with oars, Neither shall majestic ship traverse it;
22 Gama Ubangiji ne alƙalinmu, Ubangiji ne mai ba mu dokoki, Ubangiji ne sarkinmu; shi ne wanda zai cece mu.
For, Yahweh is our judge, Yahweh, is our lawgiver, —Yahweh, is our king, He will save us!
23 Maɗaurinku sun kunce ƙarfafan itacen jirgin ba su da kāriya, fikafikan jirgin ba su buɗu ba. Ta haka za a raba yalwar ganima har ma guragu za su kwashe ganimar.
Loosed are thy ropes, —They cannot strengthen the socket of their mast They have not unfurled a sail Now, can be apportioned spoil, in abundance, The lame, have captured prey!
24 Ba wani mazauna a Sihiyona da zai ce, “Ina ciwo”; za a kuma gafarta zunuban waɗanda suke zama a can.
Neither shall the inhabitant say. I am sick, —the people who dwell therein, have been forgiven iniquity.