< Ishaya 33 >

1 Kaitonka, ya kai mai hallakarwa, kai da ba a hallakar da kai ba! Kaitonka, ya maciya amana, kai da ba a ci amanarka ba! Sa’ad da ka daina hallakarwa, za a hallaka ka; sa’ad da ka daina cin amana, za a ci amanarka.
Woe, spoiler! And you not spoiled, And treacherous! And they did not deal treacherously with you, When you finish, O spoiler, you are spoiled, When you finish dealing treacherously, They deal treacherously with you.
2 Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai; muna marmarinka. Ka zama ƙarfinmu kowace safiya, cetonmu a lokacin damuwa.
O YHWH, favor us, We have waited for You, Be their arm, in the mornings, Indeed, our salvation in time of adversity.
3 Da tsawar muryarka, mutane za su gudu; sa’ad da ka tashi, al’ummai za su watse.
From the voice of a multitude peoples have fled, From Your exaltation nations have been scattered.
4 Ganimarku, ya al’ummai ƙanana fāri sun girbe; kamar tarin fārin da mutane sun fāɗa wa.
And Your spoil has been gathered, A gathering of the caterpillar, As a running to and fro of locusts He is running on it.
5 Ubangiji da girma yake, gama yana zaune a bisa; zai cika Sihiyona cikin gaskiya da adalci.
YHWH is set on high, for He is dwelling on high, He filled Zion [with] judgment and righteousness,
6 Zai zama tabbataccen harsashi na koyaushe, ma’ajin ceto da hikima da sani a yalwace; tsoron Ubangiji shi ne mabuɗin wannan dukiya.
And has been the steadfastness of your times, The strength of salvation, wisdom, and knowledge, Fear of YHWH—it [is] His treasure.
7 Duba, jarumawansu suna kuka da ƙarfi a tituna; jakadun salama suna kuka mai zafi.
Behold, “Their Ariel,” they have cried outside, Messengers of peace weep bitterly.
8 An gudu an bar manyan hanyoyi, babu matafiye a kan hanyoyi. Aka keta yarjejjeniya, an rena shaidunsa ba a kuwa ganin girman kowa.
Highways have been desolated, He who passes along the path has ceased, He has broken covenant, He has despised enemies, He has not esteemed a man.
9 Ƙasa tana kuka an kuma gudu an bar ta, Lebanon ta sha kunya ta kuma yanƙwane; Sharon ta zama kamar Araba, Bashan da Karmel sun kakkaɓe ganyayensu.
The land has mourned, languished, Lebanon has been confounded, Sharon has been withered as a wilderness, And Bashan and Carmel are shaking.
10 “Yanzu zan tashi,” in ji Ubangiji. “Yanzu ne za a ɗaukaka ni; yanzu za a ɗaga ni sama.
Now I arise, says YHWH, Now I am exalted, now I am lifted up.
11 Kun yi cikin yayi, kuka haifi kara; numfashinku wuta ne da zai cinye ku.
You conceive chaff, you bear stubble; Your spirit—a fire [that] devours you.
12 Za a ƙone mutane kamar da ƙuna farar ƙasa; kamar ƙayayyuwan da aka sare aka kuma sa musu wuta.”
And peoples have been [as] burnings of lime, Thorns, as sweepings, they burn with fire.
13 Ku da kuke da nesa, ku ji abin da na yi; ku da kuke kusa, ku san ikona!
Hear, you far off, that which I have done, And know, you near ones, My might.
14 Masu zunubi a Sihiyona sun firgita; rawar jiki ya kama marasa sanin Allah suna cewa, “Wane ne a cikinmu zai iya zama da wuta mai ci? Wane ne a cikinmu zai iya zama da madawwamiyar ƙonewa?”
Sinners have been afraid in Zion, Trembling has seized the profane: Who dwells for us—consuming fire, Who dwells for us—burnings of the age?
15 Shi da yake tafiya cikin adalci yana kuma magana abin da yake daidai, wanda yake ƙin riba daga cuta yana kuma kiyaye hannunsa daga karɓan cin hanci, wanda yake hana kunnuwansa daga ƙulla kisa ya kuma rufe idanunsa a kan tunanin aikata mugunta,
Whoever is walking righteously, And is speaking uprightly, Kicking against gain of oppressions, Shaking his hands from taking hold on a bribe, Stopping his ear from hearing of blood, And shutting his eyes from looking on evil,
16 shi ne mutumin da zai zauna a bisa, wanda mafakarsa za tă zama kagarar dutse. Za a tanada abincinsa, kuma ruwa ba zai kāsa masa ba.
He inhabits high places, Strongholds of rock [are] his high tower, His bread has been given, his waters steadfast.
17 Idanunku za su ga sarki a cikin kyansa ku kuma hangi ƙasar da take shimfiɗe can da nisa.
Your eyes see a king in his beauty, They see a far-off land.
18 Cikin tunaninku za ku yi tunani firgitar da ta faru tun dā kuna cewa, “Ina hafsan nan? Ina wannan wanda yake karɓar haraji? Ina hafsan da yake lura da hasumiyoyi?”
Your heart meditates [on] terror, Where [is] he who is counting? Where [is] he who is weighing? Where [is] he who is counting the towers?
19 Ba za ku ƙara ganin waɗannan mutane masu girman kai kuma ba, waɗannan mutane masu magana da harshen da ba ku fahimta ba.
You do not see the strong people, A people deeper of lip than to be understood, Of a scorned tongue, there is no understanding.
20 Ku duba Sihiyona, birnin shagulgulanmu; idanunku za su ga Urushalima, mazauni mai lafiya, tentin da ba za a taɓa gusar ba; wanda ba a taɓa tumɓuke turakunsa ba, ko a tsinke igiyoyinta.
See Zion, the city of our meetings, Your eyes see Jerusalem—a quiet habitation, A tent not taken down, its pins are not removed forever, And none of its cords are broken.
21 A can Ubangiji zai zama Mai Iko Duka namu. Zai zama kamar inda manyan koguna da rafuffuka suke. Matuƙan jirgin ruwa ba za su kai wurinsu ba, manyan jiragen ruwa ba za su yi zirga-zirga a kansu ba.
But YHWH [is] mighty for us there, A place of rivers—streams of broad sides, No ship with oars goes into it, And a mighty ship does not pass over it.
22 Gama Ubangiji ne alƙalinmu, Ubangiji ne mai ba mu dokoki, Ubangiji ne sarkinmu; shi ne wanda zai cece mu.
For YHWH, ours who is judging, YHWH our lawgiver, YHWH our King—He saves us.
23 Maɗaurinku sun kunce ƙarfafan itacen jirgin ba su da kāriya, fikafikan jirgin ba su buɗu ba. Ta haka za a raba yalwar ganima har ma guragu za su kwashe ganimar.
Your ropes have been left, They do not correctly strengthen their mast, They have not spread out a sail, Then a prey of much spoil has been apportioned, The lame have taken spoil.
24 Ba wani mazauna a Sihiyona da zai ce, “Ina ciwo”; za a kuma gafarta zunuban waɗanda suke zama a can.
Nor does an inhabitant say, “I was sick”; The people dwelling in it [are] forgiven of [their] iniquity!

< Ishaya 33 >