< Ishaya 33 >

1 Kaitonka, ya kai mai hallakarwa, kai da ba a hallakar da kai ba! Kaitonka, ya maciya amana, kai da ba a ci amanarka ba! Sa’ad da ka daina hallakarwa, za a hallaka ka; sa’ad da ka daina cin amana, za a ci amanarka.
Woe to thee that spoylest, and wast not spoyled: and doest wickedly, and they did not wickedly against thee: when thou shalt cease to spoyle, thou shalt be spoyled: when thou shalt make an ende of doing wickedly, they shall doe wickedly against thee.
2 Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai; muna marmarinka. Ka zama ƙarfinmu kowace safiya, cetonmu a lokacin damuwa.
O Lord, haue mercie vpon vs, wee haue waited for thee: be thou, which waste their arme in the morning, our helpe also in time of trouble.
3 Da tsawar muryarka, mutane za su gudu; sa’ad da ka tashi, al’ummai za su watse.
At the noise of the tumult, the people fled: at thine exalting the nations were scattered.
4 Ganimarku, ya al’ummai ƙanana fāri sun girbe; kamar tarin fārin da mutane sun fāɗa wa.
And your spoyle shall be gathered like the gathering of caterpillers: and he shall go against him like the leaping of grashoppers.
5 Ubangiji da girma yake, gama yana zaune a bisa; zai cika Sihiyona cikin gaskiya da adalci.
The Lord is exalted: for hee dwelleth on hie: he hath filled Zion with iudgement and iustice.
6 Zai zama tabbataccen harsashi na koyaushe, ma’ajin ceto da hikima da sani a yalwace; tsoron Ubangiji shi ne mabuɗin wannan dukiya.
And there shall be stabilitie of thy times, strength, saluation, wisdome and knowledge: for the feare of the Lord shalbe his treasure.
7 Duba, jarumawansu suna kuka da ƙarfi a tituna; jakadun salama suna kuka mai zafi.
Behold, their messengers shall cry without, and ye ambassadours of peace shall weepe bitterly.
8 An gudu an bar manyan hanyoyi, babu matafiye a kan hanyoyi. Aka keta yarjejjeniya, an rena shaidunsa ba a kuwa ganin girman kowa.
The pathes are waste: the wayfaring man ceaseth: hee hath broken the couenant: hee hath contemned the cities: he regarded no man.
9 Ƙasa tana kuka an kuma gudu an bar ta, Lebanon ta sha kunya ta kuma yanƙwane; Sharon ta zama kamar Araba, Bashan da Karmel sun kakkaɓe ganyayensu.
The earth mourneth and fainteth: Lebanon is ashamed, and hewen downe: Sharon is like a wildernes, and Bashan is shaken and Carmel.
10 “Yanzu zan tashi,” in ji Ubangiji. “Yanzu ne za a ɗaukaka ni; yanzu za a ɗaga ni sama.
Now will I arise, saith the Lord: now will I be exalted, now will I lift vp my selfe.
11 Kun yi cikin yayi, kuka haifi kara; numfashinku wuta ne da zai cinye ku.
Ye shall conceiue chaffe, and bring forth stubble: the fire of your breath shall deuoure you.
12 Za a ƙone mutane kamar da ƙuna farar ƙasa; kamar ƙayayyuwan da aka sare aka kuma sa musu wuta.”
And the people shall be as the burning of lime: and as the thornes cut vp, shall they be burnt in the fire.
13 Ku da kuke da nesa, ku ji abin da na yi; ku da kuke kusa, ku san ikona!
Heare, yee that are farre off, what I haue done, and ye that are neere, know my power.
14 Masu zunubi a Sihiyona sun firgita; rawar jiki ya kama marasa sanin Allah suna cewa, “Wane ne a cikinmu zai iya zama da wuta mai ci? Wane ne a cikinmu zai iya zama da madawwamiyar ƙonewa?”
The sinners in Zion are afraide: a feare is come vpon the hypocrites: who among vs shall dwel with the deuouring fire? who among vs shall dwell with the euerlasting burnings?
15 Shi da yake tafiya cikin adalci yana kuma magana abin da yake daidai, wanda yake ƙin riba daga cuta yana kuma kiyaye hannunsa daga karɓan cin hanci, wanda yake hana kunnuwansa daga ƙulla kisa ya kuma rufe idanunsa a kan tunanin aikata mugunta,
Hee that walketh in iustice, and speaketh righteous things, refusing gaine of oppression, shaking his handes from taking of gifts, stopping his eares from hearing of blood, and shutting his eyes from seeing euill.
16 shi ne mutumin da zai zauna a bisa, wanda mafakarsa za tă zama kagarar dutse. Za a tanada abincinsa, kuma ruwa ba zai kāsa masa ba.
He shall dwell on hie: his defence shall be the munitions of rockes: bread shalbe giuen him, and his waters shalbe sure.
17 Idanunku za su ga sarki a cikin kyansa ku kuma hangi ƙasar da take shimfiɗe can da nisa.
Thine eyes shall see the King in his glory: they shall beholde the lande farre off.
18 Cikin tunaninku za ku yi tunani firgitar da ta faru tun dā kuna cewa, “Ina hafsan nan? Ina wannan wanda yake karɓar haraji? Ina hafsan da yake lura da hasumiyoyi?”
Thine heart shall meditate feare, Where is the scribe? where is the receiuer? where is hee that counted the towres?
19 Ba za ku ƙara ganin waɗannan mutane masu girman kai kuma ba, waɗannan mutane masu magana da harshen da ba ku fahimta ba.
Thou shalt not see a fierce people, a people of a darke speache, that thou canst not perceiue, and of a stammering tongue that thou canst not vnderstande.
20 Ku duba Sihiyona, birnin shagulgulanmu; idanunku za su ga Urushalima, mazauni mai lafiya, tentin da ba za a taɓa gusar ba; wanda ba a taɓa tumɓuke turakunsa ba, ko a tsinke igiyoyinta.
Looke vpon Zion the citie of our solemne feastes: thine eyes shall see Ierusalem a quiet habitation, a Tabernacle that can not be remooued: and the stakes thereof can neuer be taken away, neither shall any of the cordes thereof be broken.
21 A can Ubangiji zai zama Mai Iko Duka namu. Zai zama kamar inda manyan koguna da rafuffuka suke. Matuƙan jirgin ruwa ba za su kai wurinsu ba, manyan jiragen ruwa ba za su yi zirga-zirga a kansu ba.
For surely there the mightie Lord will be vnto vs, as a place of floods and broade riuers, whereby shall passe no shippe with oares, neither shall great shippe passe thereby.
22 Gama Ubangiji ne alƙalinmu, Ubangiji ne mai ba mu dokoki, Ubangiji ne sarkinmu; shi ne wanda zai cece mu.
For the Lord is our Iudge, the Lord is our lawe giuer: the Lord is our King, he will saue vs.
23 Maɗaurinku sun kunce ƙarfafan itacen jirgin ba su da kāriya, fikafikan jirgin ba su buɗu ba. Ta haka za a raba yalwar ganima har ma guragu za su kwashe ganimar.
Thy cordes are loosed: they could not well strengthen their maste, neither coulde they spread the saile: then shall the praye be deuided for a great spoile: yea, the lame shall take away the pray.
24 Ba wani mazauna a Sihiyona da zai ce, “Ina ciwo”; za a kuma gafarta zunuban waɗanda suke zama a can.
And none inhabitant shall say, I am sicke: the people that dwell therein, shall haue their iniquitie forgiuen.

< Ishaya 33 >