< Ishaya 33 >
1 Kaitonka, ya kai mai hallakarwa, kai da ba a hallakar da kai ba! Kaitonka, ya maciya amana, kai da ba a ci amanarka ba! Sa’ad da ka daina hallakarwa, za a hallaka ka; sa’ad da ka daina cin amana, za a ci amanarka.
Tragedy is coming to you, you destroyer who has not experienced destruction yourself, you deceiver who has not experienced deception yourself! When you have finished with your destroying, you will be destroyed yourself. Then you are finished with your deceiving, you will be deceived yourselves.
2 Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai; muna marmarinka. Ka zama ƙarfinmu kowace safiya, cetonmu a lokacin damuwa.
Lord, please be kind to us; we put our confidence in you. Be the strength we rely on every morning; be our salvation in times of trouble.
3 Da tsawar muryarka, mutane za su gudu; sa’ad da ka tashi, al’ummai za su watse.
When you roar, the peoples run away; when you prepare for action, the nations scatter!
4 Ganimarku, ya al’ummai ƙanana fāri sun girbe; kamar tarin fārin da mutane sun fāɗa wa.
You plunder defeated enemy armies like caterpillars eating up plants; like an attack of swarming locusts.
5 Ubangiji da girma yake, gama yana zaune a bisa; zai cika Sihiyona cikin gaskiya da adalci.
The Lord is praised for he lives in highest heaven; he has filled Zion with justice and right.
6 Zai zama tabbataccen harsashi na koyaushe, ma’ajin ceto da hikima da sani a yalwace; tsoron Ubangiji shi ne mabuɗin wannan dukiya.
He will be your constant support throughout your lives an abundant source of salvation, wisdom, and knowledge. Reverence for the Lord is what makes Zion rich.
7 Duba, jarumawansu suna kuka da ƙarfi a tituna; jakadun salama suna kuka mai zafi.
But look! Even your bravest soldiers are crying loudly in the street; the messengers you sent to ask for peace are weeping bitterly.
8 An gudu an bar manyan hanyoyi, babu matafiye a kan hanyoyi. Aka keta yarjejjeniya, an rena shaidunsa ba a kuwa ganin girman kowa.
Your highways are deserted; nobody's traveling on your roads anymore. He breaks the treaty; he despises the witnesses; he doesn't care about anybody.
9 Ƙasa tana kuka an kuma gudu an bar ta, Lebanon ta sha kunya ta kuma yanƙwane; Sharon ta zama kamar Araba, Bashan da Karmel sun kakkaɓe ganyayensu.
Israel is in mourning and fades away; Lebanon withers in shame; the fields of Sharon have become a desert; the forests of Bashan and Carmel have shed their leaves.
10 “Yanzu zan tashi,” in ji Ubangiji. “Yanzu ne za a ɗaukaka ni; yanzu za a ɗaga ni sama.
“But now I'm going to intervene!” says the Lord. “I'm prepared to act! I will show myself to be above all others!
11 Kun yi cikin yayi, kuka haifi kara; numfashinku wuta ne da zai cinye ku.
All you give birth to is only dry grass, all you deliver is just stubble. Your breath is a fire that will burn you up.
12 Za a ƙone mutane kamar da ƙuna farar ƙasa; kamar ƙayayyuwan da aka sare aka kuma sa musu wuta.”
You people will be burned to ashes like thorns that are cut down and thrown into the fire.
13 Ku da kuke da nesa, ku ji abin da na yi; ku da kuke kusa, ku san ikona!
Those of you who are far away, recognize what I have accomplished; those of you who are nearby, recognize how powerful I am.”
14 Masu zunubi a Sihiyona sun firgita; rawar jiki ya kama marasa sanin Allah suna cewa, “Wane ne a cikinmu zai iya zama da wuta mai ci? Wane ne a cikinmu zai iya zama da madawwamiyar ƙonewa?”
The sinners who live in Zion tremble with fear; those who are irreligious are overcome with terror. They ask, “Who can live with this fire that consumes everything? Who can live among such everlasting burning?”
15 Shi da yake tafiya cikin adalci yana kuma magana abin da yake daidai, wanda yake ƙin riba daga cuta yana kuma kiyaye hannunsa daga karɓan cin hanci, wanda yake hana kunnuwansa daga ƙulla kisa ya kuma rufe idanunsa a kan tunanin aikata mugunta,
Those who live right and speak the truth, those who refuse to profit from extortion and refuse to take bribes, who don't listen to plots to kill people, who close their eyes rather than look at evil.
16 shi ne mutumin da zai zauna a bisa, wanda mafakarsa za tă zama kagarar dutse. Za a tanada abincinsa, kuma ruwa ba zai kāsa masa ba.
They will live on high; they will be protected by the mountain fortresses; they will always be provided with food and will always have water.
17 Idanunku za su ga sarki a cikin kyansa ku kuma hangi ƙasar da take shimfiɗe can da nisa.
You will see the king in his wonderful appearance, and you will view a land that stretches into the distance.
18 Cikin tunaninku za ku yi tunani firgitar da ta faru tun dā kuna cewa, “Ina hafsan nan? Ina wannan wanda yake karɓar haraji? Ina hafsan da yake lura da hasumiyoyi?”
In your mind you will think about the terrifying things that were expected, and then ask yourself, “Where are the enemy officials—the scribes who were to record events, the treasurers who were to weigh the looted money, the surveyors who were to count and destroy the towers?”
19 Ba za ku ƙara ganin waɗannan mutane masu girman kai kuma ba, waɗannan mutane masu magana da harshen da ba ku fahimta ba.
You won't see these offensive people anymore with their barbaric language that sounds like someone stammering and is impossible to understand.
20 Ku duba Sihiyona, birnin shagulgulanmu; idanunku za su ga Urushalima, mazauni mai lafiya, tentin da ba za a taɓa gusar ba; wanda ba a taɓa tumɓuke turakunsa ba, ko a tsinke igiyoyinta.
On the contrary, you'll see Zion as a festival city. You will view Jerusalem as a quiet and peaceful place. It will be like a tent that's never taken down, whose tent-pegs are never pulled up, whose guy ropes never snap.
21 A can Ubangiji zai zama Mai Iko Duka namu. Zai zama kamar inda manyan koguna da rafuffuka suke. Matuƙan jirgin ruwa ba za su kai wurinsu ba, manyan jiragen ruwa ba za su yi zirga-zirga a kansu ba.
Right here our majestic Lord will be like a place of broad rivers and waters that no enemy ship with oars can cross—no great ship can pass.
22 Gama Ubangiji ne alƙalinmu, Ubangiji ne mai ba mu dokoki, Ubangiji ne sarkinmu; shi ne wanda zai cece mu.
For the Lord is our judge, the Lord is our lawgiver, the Lord is our king. He is the one who will save us.
23 Maɗaurinku sun kunce ƙarfafan itacen jirgin ba su da kāriya, fikafikan jirgin ba su buɗu ba. Ta haka za a raba yalwar ganima har ma guragu za su kwashe ganimar.
The rigging on your ship hangs loose so the mast isn't secure and the sail can't be spread. Then all the looted treasure you're carrying will be divided among the victors—even those who are lame will have their share.
24 Ba wani mazauna a Sihiyona da zai ce, “Ina ciwo”; za a kuma gafarta zunuban waɗanda suke zama a can.
Nobody in Israel will say, “I'm sick,” and those who live there will have their guilt removed.