< Ishaya 32 >

1 Duba, sarki zai yi mulki cikin adalci masu mulki kuma su yi mulki da adalci.
A IA hoi, ma ka pono no e malama aupuni ai ke alii nui, A ma ka pololei hoi e noho alii ai na'lii.
2 Kowane mutum zai zama kamar wurin fakewa daga iska mafaka kuma daga hadari, kamar rafuffukan ruwa a hamada da kuma inuwar babban dutse a ƙeƙasasshiyar ƙasa.
E like auanei ke kanaka me kahi lulu o ka makani, Me ka mamalu hoi no ka ua; E like me na auwai ma kahi maloo, E like hoi me ka malu o ka pohaku nui ma ka aina maluhiluhi.
3 Sa’an nan idanun waɗanda suka gani ba za su ƙara rufewa ba, kunnuwan waɗanda suka ji kuma za su saurara.
Aole e hoopiliia na maka o ka poe ike, A e hoolohe no na pepeiao o ka poe lohe.
4 Zuciya marasa haƙuri za su sani su kuma fahimta, harshen masu ana’ana kuma zai sāke su yi magana sosai.
E ike no hoi ka naau o ka poe noonoo ole i ke akamai, A o ke alelo o ka poe uuu, E makaukau no ia e olelo akaka mai.
5 Ba za a ƙara ce da wawa mai girma ba ko kuwa a ɗaukaka mazambaci.
Aole e kapa hou ia ka mea lapuwale, he maikai nui, Aole hoi e iia ka mea alunu, he lokomaikai.
6 Gama wawa maganar wauta yakan yi, zuciyarsa ta cika da mugunta, yana aikata abubuwan rashin sanin Allah yana baza kurakurai game da Ubangiji; yana barin mayunwata da yunwa ya kuma hana masu ƙishirwa ruwan sha.
No ka mea, e olelo no ke kanaka lapuwale i ka mea lapuwale, A e ohumu no kona naau i ka hewa, Ma ka aia kana hana ana, a olelo ino ku e ia Iehova, E hoonele i ka naau o ka poe pololi. A e hoopau i ka wai o ka mea makewai.
7 Matakan mazambaci mugaye ne, yana ƙulla mugayen shirye-shirye don yă hallaka talakawa da ƙarairayi, ko sa’ad da roƙon mai bukata da gaskiya ne.
He hewa na mea hana o ka mea alunu; Imi no oia i na manao hewa, E hookaumaha i ka poe poino i na olelo wahahee, I ka poe popilikia hoi e olelo ana ma ka pololei.
8 Amma mutumin kirki kan yi shirye-shirye masu kirki, kuma yakan tsaya a kan ayyukan kirki.
Aka, o ka mea lokomaikai, imi no oia i ka lokomaikai, A ma ka lokomaikai oia e kupaa ai.
9 Ku matan da kuke zaman jin daɗi, ku tashi ku saurare ni; ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya, ku ji abin da zan faɗa!
E na wahine e noho nanea ana, E ku mai iluna, e hoolohe hoi i ko'u leo; E na kaikamahine makau ole, e haliu pepeiao mai i ka'u olelo.
10 Cikin ɗan lokaci ƙasa da shekara guda ku da kuke tsammani kuna da kāriya za ku yi rawar jiki; girbin’ya’yan inabi zai kāsa, girbin’ya’yan itatuwa kuma ba zai zo ba.
No ka makahiki a keu ko oukou haalulu ana, E na wahine makau ole; No ka mea, e pau auanei ka ohi hua waina ana, Aole e hiki mai ka hooiliili ai ana.
11 Ku yi rawar jiki, ku mata masu jin daɗi, ku sha wahala, ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya! Ku tuɓe rigunanku, ku ɗaura tsummoki a kwankwasonku.
E haalulu oukou, e ka poe e noho nanea ana, E weliweli hoi oukou, ka poe makau ole; E wehe i ko oukou lole, a e ku kohana, a e kaei i na puhaka.
12 Ku bugi ƙirjinku don gonaki masu kyau don’ya’yan inabi
E nui auanei ka uwe ana no na waiu, A no na mahinaai maikai, a no ke kumuwaina hua nui.
13 da kuma don ƙasar mutanena, da ƙasar da ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suka yi girma, I, ku yi kuka saboda dukan gidajen da dā ake biki da kuma domin wannan birnin da dā ake murna a ciki.
Ma ka aina o ko'u poe kanaka, E ulu mai no ke kakalaioa, a me ka laau ooi, Maluna hoi o na hale olioli a pau, Iloko o ke kulanakauhale e olioli ana.
14 Za a ƙyale kagarar, a gudu a bar birnin da dā ake hayaniya; mafaka da hasumiyar tsaro za su zama kango har abada, jin daɗin jakuna, makiyaya don garkuna,
No ka mea, e haaleleia auanei na halealii, A e neoneo no hoi ke kulanakauhale o na kanaka lehulehu; O ka puu a me ka halekiai e lilo no i ana mau loa, I mea hoi e olioli ai na hoki hihiu, I wahi hoi e hanai ai i na holoholona;
15 sai an zubo Ruhu a kanmu daga sama, hamada kuma ta zama ƙasar mai taƙi, gona mai taƙi kuma ta zama kamar kurmi.
A nininiia ka Uhane mailuna mai maluna o kakou, A lilo ka waonahele i mahinaai hua nui, A manaoia hoi ka mahinaai hua nui, he ululaau.
16 Aikin gaskiya zai zauna a hamada adalci kuma zai zauna a ƙasa mai taƙi.
Alaila, e noho no ka pono ma ka waonahele, A e hoomau no hoi ka maikai ma ka mahinaai hua nui.
17 Aikin adalci zai zama salama; tasirin adalci zai zama natsuwa da tabbaci har abada.
E lilo no ka hana pono ana i mea e malu ai, A o ka hope o ka maikai, he kuapapanui mau loa, a me ka malu.
18 Mutanena za su zauna lafiya a wuraren salama, a gidaje masu kāriya, a wuraren hutun da babu fitina.
E noho no ko'u poe kanaka ma na wahi kuapapanui, A ma na hale hoi i hoomaluia, A ma na wahi hoomaha o ka malu.
19 Ko da yake ƙanƙara za tă fāɗo a jeji, a kuma rurrushe birni gaba ɗaya,
Aka, e haule mai no ka hua hekili, I ke kuaia ilalo o ka ululaau; A i kahi haahaa e hoohaahaaia'i ke kulanakauhale.
20 zai zama muku da albarka, ku da kuke shuki iri kusa da kowane rafi, kuna kuma barin lafiyayyiyar makiyaya domin shanu da jakunanku.
E pomaikai auanei oukou, ka poe lulu hua ma na wahi wai nui, Ma kahi i hoounaia'i ka bipi kaulua a me ka hoki.

< Ishaya 32 >