< Ishaya 32 >

1 Duba, sarki zai yi mulki cikin adalci masu mulki kuma su yi mulki da adalci.
Voici le roi régnera selon la justice, les princes gouverneront avec équité.
2 Kowane mutum zai zama kamar wurin fakewa daga iska mafaka kuma daga hadari, kamar rafuffukan ruwa a hamada da kuma inuwar babban dutse a ƙeƙasasshiyar ƙasa.
Et chacun d'eux sera comme un abri contre le vent et un refuge contre la pluie, comme des ruisseaux d'eau dans une terre aride, comme l'ombre d'un grand rocher dans un pays désolé.
3 Sa’an nan idanun waɗanda suka gani ba za su ƙara rufewa ba, kunnuwan waɗanda suka ji kuma za su saurara.
Alors les yeux de ceux qui voient ne seront plus couverts, et les oreilles de ceux qui entendent seront attentives.
4 Zuciya marasa haƙuri za su sani su kuma fahimta, harshen masu ana’ana kuma zai sāke su yi magana sosai.
Le cœur des hommes légers entendra la sagesse; la langue des bègues parlera promptement et nettement.
5 Ba za a ƙara ce da wawa mai girma ba ko kuwa a ɗaukaka mazambaci.
L'insensé ne sera plus appelé noble, et le trompeur ne sera plus nommé magnifique.
6 Gama wawa maganar wauta yakan yi, zuciyarsa ta cika da mugunta, yana aikata abubuwan rashin sanin Allah yana baza kurakurai game da Ubangiji; yana barin mayunwata da yunwa ya kuma hana masu ƙishirwa ruwan sha.
Car l'insensé ne prononce que folie, et son cœur s'adonne à la fausseté, pour commettre l'impiété, pour blasphémer contre l'Éternel, pour frustrer l'âme de l'affamé, et pour ôter le breuvage à celui qui a soif.
7 Matakan mazambaci mugaye ne, yana ƙulla mugayen shirye-shirye don yă hallaka talakawa da ƙarairayi, ko sa’ad da roƙon mai bukata da gaskiya ne.
Quant au trompeur, ses moyens sont pernicieux; il trouve des inventions pour perdre les affligés par des paroles fausses, et le pauvre dont la cause est juste.
8 Amma mutumin kirki kan yi shirye-shirye masu kirki, kuma yakan tsaya a kan ayyukan kirki.
Mais l'homme noble forme de nobles desseins, et il se lève pour agir avec noblesse.
9 Ku matan da kuke zaman jin daɗi, ku tashi ku saurare ni; ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya, ku ji abin da zan faɗa!
Femmes insouciantes, levez-vous, écoutez ma voix! Filles qui vous tenez assurées, prêtez l'oreille à ma parole!
10 Cikin ɗan lokaci ƙasa da shekara guda ku da kuke tsammani kuna da kāriya za ku yi rawar jiki; girbin’ya’yan inabi zai kāsa, girbin’ya’yan itatuwa kuma ba zai zo ba.
Dans un an et quelques jours vous tremblerez, vous qui êtes assurées; car la vendange aura manqué, on ne fera point de récolte.
11 Ku yi rawar jiki, ku mata masu jin daɗi, ku sha wahala, ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya! Ku tuɓe rigunanku, ku ɗaura tsummoki a kwankwasonku.
Soyez dans l'effroi, insouciantes! Tremblez, vous qui êtes assurées! Dépouillez-vous, mettez-vous à nu, ceignez vos reins pour le deuil!
12 Ku bugi ƙirjinku don gonaki masu kyau don’ya’yan inabi
Frappez-vous la poitrine, à cause des belles campagnes et des vignes fertiles.
13 da kuma don ƙasar mutanena, da ƙasar da ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suka yi girma, I, ku yi kuka saboda dukan gidajen da dā ake biki da kuma domin wannan birnin da dā ake murna a ciki.
Les épines, les ronces monteront sur la terre de mon peuple, même sur toutes les maisons de plaisance de la cité joyeuse.
14 Za a ƙyale kagarar, a gudu a bar birnin da dā ake hayaniya; mafaka da hasumiyar tsaro za su zama kango har abada, jin daɗin jakuna, makiyaya don garkuna,
Car le palais est abandonné; la ville bruyante est délaissée; la colline et la tour sont à jamais comme des cavernes; les ânes sauvages s'y joueront, et les troupeaux y paîtront;
15 sai an zubo Ruhu a kanmu daga sama, hamada kuma ta zama ƙasar mai taƙi, gona mai taƙi kuma ta zama kamar kurmi.
Jusqu'à ce que l'Esprit soit répandu sur nous d'en haut, que le désert devienne un verger, et que le verger soit semblable à une forêt.
16 Aikin gaskiya zai zauna a hamada adalci kuma zai zauna a ƙasa mai taƙi.
Alors l'équité habitera dans le désert, et la justice fera sa demeure dans le verger.
17 Aikin adalci zai zama salama; tasirin adalci zai zama natsuwa da tabbaci har abada.
La justice produira la paix, et le fruit de la justice sera le repos et la sûreté pour toujours.
18 Mutanena za su zauna lafiya a wuraren salama, a gidaje masu kāriya, a wuraren hutun da babu fitina.
Mon peuple habitera une demeure paisible, des habitations sûres et des asiles tranquilles.
19 Ko da yake ƙanƙara za tă fāɗo a jeji, a kuma rurrushe birni gaba ɗaya,
Mais la forêt tombera sous la grêle, et la ville sera entièrement abaissée.
20 zai zama muku da albarka, ku da kuke shuki iri kusa da kowane rafi, kuna kuma barin lafiyayyiyar makiyaya domin shanu da jakunanku.
Heureux, vous qui semez près de toutes les eaux, qui y faites mouvoir le pied du bœuf et de l'âne!

< Ishaya 32 >