< Ishaya 32 >
1 Duba, sarki zai yi mulki cikin adalci masu mulki kuma su yi mulki da adalci.
Voici, un Roi régnera en justice, et les Princes présideront avec équité.
2 Kowane mutum zai zama kamar wurin fakewa daga iska mafaka kuma daga hadari, kamar rafuffukan ruwa a hamada da kuma inuwar babban dutse a ƙeƙasasshiyar ƙasa.
Et ce personnage sera comme le lieu auquel on se retire à couvert du vent, et comme un asile contre la tempête; comme [sont] les ruisseaux d'eaux dans un pays sec, et l'ombre d'un gros rocher en une terre altérée.
3 Sa’an nan idanun waɗanda suka gani ba za su ƙara rufewa ba, kunnuwan waɗanda suka ji kuma za su saurara.
Alors les yeux de ceux qui voient, ne seront point retenus; et les oreilles de ceux qui entendent, seront attentives.
4 Zuciya marasa haƙuri za su sani su kuma fahimta, harshen masu ana’ana kuma zai sāke su yi magana sosai.
Et le cœur des étourdis entendra la science; et la langue des bègues parlera aisément, et nettement.
5 Ba za a ƙara ce da wawa mai girma ba ko kuwa a ɗaukaka mazambaci.
Le chiche ne sera plus appelé libéral, et l'avare ne sera plus nommé magnifique.
6 Gama wawa maganar wauta yakan yi, zuciyarsa ta cika da mugunta, yana aikata abubuwan rashin sanin Allah yana baza kurakurai game da Ubangiji; yana barin mayunwata da yunwa ya kuma hana masu ƙishirwa ruwan sha.
Car le chiche ne prononce que chicheté, et son cœur ne machine qu'iniquité, pour exécuter son déguisement, et pour proférer des choses fausses contre l'Eternel; pour rendre vide l'âme de l'affamé, et faire tarir la boisson à celui qui a soif.
7 Matakan mazambaci mugaye ne, yana ƙulla mugayen shirye-shirye don yă hallaka talakawa da ƙarairayi, ko sa’ad da roƙon mai bukata da gaskiya ne.
Les instruments de l'avare sont pernicieux; il prend des conseils pleins de machinations, pour attraper par des paroles de mensonge les affligés, même quand le pauvre parle droitement.
8 Amma mutumin kirki kan yi shirye-shirye masu kirki, kuma yakan tsaya a kan ayyukan kirki.
Mais le libéral prend des conseils de libéralité, et se lève pour user de libéralité.
9 Ku matan da kuke zaman jin daɗi, ku tashi ku saurare ni; ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya, ku ji abin da zan faɗa!
Femmes qui êtes à votre aise, levez-vous, écoutez ma voix; filles qui vous tenez assurées, prêtez l'oreille à ma parole.
10 Cikin ɗan lokaci ƙasa da shekara guda ku da kuke tsammani kuna da kāriya za ku yi rawar jiki; girbin’ya’yan inabi zai kāsa, girbin’ya’yan itatuwa kuma ba zai zo ba.
Dans un an et quelques jours au delà, vous qui vous tenez assurées, serez troublées; car la vendange a manqué; la récolte ne viendra plus.
11 Ku yi rawar jiki, ku mata masu jin daɗi, ku sha wahala, ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya! Ku tuɓe rigunanku, ku ɗaura tsummoki a kwankwasonku.
Vous qui êtes à votre aise, tremblez; vous qui vous tenez assurées, soyez troublées; dépouillez-vous, quittez vos habits, et vous ceignez [de sacs] sur les reins.
12 Ku bugi ƙirjinku don gonaki masu kyau don’ya’yan inabi
On se frappe la poitrine, à cause de la vigne abondante en fruit.
13 da kuma don ƙasar mutanena, da ƙasar da ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suka yi girma, I, ku yi kuka saboda dukan gidajen da dā ake biki da kuma domin wannan birnin da dā ake murna a ciki.
Les épines et les ronces monteront sur la terre de mon peuple; même sur toutes les maisons où il y a de la joie, et sur la ville qui s'égaye.
14 Za a ƙyale kagarar, a gudu a bar birnin da dā ake hayaniya; mafaka da hasumiyar tsaro za su zama kango har abada, jin daɗin jakuna, makiyaya don garkuna,
Car le palais s'en va être abandonné; la multitude de la cité s'en va être délaissée; les lieux inacceccibles du pays et les forteresses seront autant de cavernes à toujours; là se joueront les ânes sauvages, et les petits y paîtront.
15 sai an zubo Ruhu a kanmu daga sama, hamada kuma ta zama ƙasar mai taƙi, gona mai taƙi kuma ta zama kamar kurmi.
Jusqu'à ce que l'Esprit soit versé d'en haut sur nous; et que le désert devienne un Carmel, et que Carmel soit réputé comme une forêt.
16 Aikin gaskiya zai zauna a hamada adalci kuma zai zauna a ƙasa mai taƙi.
Le jugement habitera au désert, et la justice se tiendra en Carmel.
17 Aikin adalci zai zama salama; tasirin adalci zai zama natsuwa da tabbaci har abada.
La paix sera l'effet de la justice, et le labourage de la justice sera le repos et la sûreté, jusques à toujours.
18 Mutanena za su zauna lafiya a wuraren salama, a gidaje masu kāriya, a wuraren hutun da babu fitina.
Et mon peuple habitera en un logis paisible, et dans des pavillons assurés, et dans un repos fort tranquille.
19 Ko da yake ƙanƙara za tă fāɗo a jeji, a kuma rurrushe birni gaba ɗaya,
Mais la grêle tombera sur la forêt, et la ville sera entièrement abaissée.
20 zai zama muku da albarka, ku da kuke shuki iri kusa da kowane rafi, kuna kuma barin lafiyayyiyar makiyaya domin shanu da jakunanku.
O que vous êtes heureux, vous qui semez sur toutes les eaux, et qui y faites aller le pied du bœuf et de l'âne!