< Ishaya 32 >
1 Duba, sarki zai yi mulki cikin adalci masu mulki kuma su yi mulki da adalci.
Voici un roi qui régnera dans la justice, et les princes gouverneront dans la justice.
2 Kowane mutum zai zama kamar wurin fakewa daga iska mafaka kuma daga hadari, kamar rafuffukan ruwa a hamada da kuma inuwar babban dutse a ƙeƙasasshiyar ƙasa.
L'homme sera comme une cachette contre le vent, et un abri de la tempête, comme des ruisseaux d'eau dans un endroit sec, comme l'ombre d'un grand rocher dans une terre épuisée.
3 Sa’an nan idanun waɗanda suka gani ba za su ƙara rufewa ba, kunnuwan waɗanda suka ji kuma za su saurara.
Les yeux de ceux qui voient ne s'obscurcissent pas, et les oreilles de ceux qui entendent écouteront.
4 Zuciya marasa haƙuri za su sani su kuma fahimta, harshen masu ana’ana kuma zai sāke su yi magana sosai.
Le cœur de l'impétueux comprendra la connaissance, et la langue des bègues sera prête à parler clairement.
5 Ba za a ƙara ce da wawa mai girma ba ko kuwa a ɗaukaka mazambaci.
L'insensé ne sera plus appelé noble, ni le scélérat être hautement respecté.
6 Gama wawa maganar wauta yakan yi, zuciyarsa ta cika da mugunta, yana aikata abubuwan rashin sanin Allah yana baza kurakurai game da Ubangiji; yana barin mayunwata da yunwa ya kuma hana masu ƙishirwa ruwan sha.
Car l'insensé dira des folies, et son cœur commettra l'iniquité, de pratiquer le blasphème, et de proférer des erreurs contre Yahvé, pour vider l'âme de ceux qui ont faim, et de faire manquer le breuvage des assoiffés.
7 Matakan mazambaci mugaye ne, yana ƙulla mugayen shirye-shirye don yă hallaka talakawa da ƙarairayi, ko sa’ad da roƙon mai bukata da gaskiya ne.
Les voies du scélérat sont mauvaises. Il élabore des plans méchants pour détruire les humbles par des paroles mensongères, même quand le nécessiteux parle juste.
8 Amma mutumin kirki kan yi shirye-shirye masu kirki, kuma yakan tsaya a kan ayyukan kirki.
Mais le noble conçoit des choses nobles, et il continuera dans les choses nobles.
9 Ku matan da kuke zaman jin daɗi, ku tashi ku saurare ni; ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya, ku ji abin da zan faɗa!
Levez-vous, femmes qui êtes à l'aise! Entendez ma voix! Filles insouciantes, écoutez mon discours!
10 Cikin ɗan lokaci ƙasa da shekara guda ku da kuke tsammani kuna da kāriya za ku yi rawar jiki; girbin’ya’yan inabi zai kāsa, girbin’ya’yan itatuwa kuma ba zai zo ba.
Pendant des jours au-delà d'une année, vous serez troublées, femmes insouciantes; pour le millésime échouera. La récolte ne viendra pas.
11 Ku yi rawar jiki, ku mata masu jin daɗi, ku sha wahala, ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya! Ku tuɓe rigunanku, ku ɗaura tsummoki a kwankwasonku.
Tremblez, vous les femmes qui êtes à l'aise! Soyez inquiets, bande d'insouciants! Déshabillez-vous, mettez-vous à nu, et mettez un sac sur votre taille.
12 Ku bugi ƙirjinku don gonaki masu kyau don’ya’yan inabi
Battez vos poitrines pour les champs agréables, pour la vigne féconde.
13 da kuma don ƙasar mutanena, da ƙasar da ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suka yi girma, I, ku yi kuka saboda dukan gidajen da dā ake biki da kuma domin wannan birnin da dā ake murna a ciki.
Les épines et les ronces pousseront sur la terre de mon peuple; oui, sur toutes les maisons de joie de la ville joyeuse.
14 Za a ƙyale kagarar, a gudu a bar birnin da dā ake hayaniya; mafaka da hasumiyar tsaro za su zama kango har abada, jin daɗin jakuna, makiyaya don garkuna,
Car le palais sera abandonné. La ville populeuse sera déserte. La colline et la tour de guet seront pour toujours des repaires, un délice pour les ânes sauvages, un pâturage de troupeaux,
15 sai an zubo Ruhu a kanmu daga sama, hamada kuma ta zama ƙasar mai taƙi, gona mai taƙi kuma ta zama kamar kurmi.
jusqu'à ce que l'Esprit soit répandu sur nous d'en haut, et le désert devient un champ fertile, et le champ fructueux est considéré comme une forêt.
16 Aikin gaskiya zai zauna a hamada adalci kuma zai zauna a ƙasa mai taƙi.
Alors la justice habitera dans le désert; et la justice restera dans le champ fructueux.
17 Aikin adalci zai zama salama; tasirin adalci zai zama natsuwa da tabbaci har abada.
L'œuvre de la justice sera la paix, et l'effet de la justice, la tranquillité et la confiance pour toujours.
18 Mutanena za su zauna lafiya a wuraren salama, a gidaje masu kāriya, a wuraren hutun da babu fitina.
Mon peuple vivra dans une demeure paisible, dans des logements sûrs, et dans des lieux de repos tranquilles,
19 Ko da yake ƙanƙara za tă fāɗo a jeji, a kuma rurrushe birni gaba ɗaya,
bien que la grêle aplatisse la forêt, et la ville est complètement rasée.
20 zai zama muku da albarka, ku da kuke shuki iri kusa da kowane rafi, kuna kuma barin lafiyayyiyar makiyaya domin shanu da jakunanku.
Heureux ceux qui sèment près de toutes les eaux! qui envoie les pieds du bœuf et de l'âne.