< Ishaya 32 >

1 Duba, sarki zai yi mulki cikin adalci masu mulki kuma su yi mulki da adalci.
Behold! a king shall reign in righteousness, And princes shall rule with equity.
2 Kowane mutum zai zama kamar wurin fakewa daga iska mafaka kuma daga hadari, kamar rafuffukan ruwa a hamada da kuma inuwar babban dutse a ƙeƙasasshiyar ƙasa.
Every one of them shall be a hiding-place from the wind, And a shelter from the tempest; As streams of water in a dry place, As the shadow of a great rock in a weary land.
3 Sa’an nan idanun waɗanda suka gani ba za su ƙara rufewa ba, kunnuwan waɗanda suka ji kuma za su saurara.
The eyes of them that see shall no more be blind, And the ears of them that hear shall hearken.
4 Zuciya marasa haƙuri za su sani su kuma fahimta, harshen masu ana’ana kuma zai sāke su yi magana sosai.
The heart of the rash shall gain wisdom, And the tongue of the stammerer learn to speak plainly.
5 Ba za a ƙara ce da wawa mai girma ba ko kuwa a ɗaukaka mazambaci.
The vile shall no more be called liberal, Nor the niggard said to be bountiful;
6 Gama wawa maganar wauta yakan yi, zuciyarsa ta cika da mugunta, yana aikata abubuwan rashin sanin Allah yana baza kurakurai game da Ubangiji; yana barin mayunwata da yunwa ya kuma hana masu ƙishirwa ruwan sha.
For the vile will still utter villany, And his heart will devise iniquity; He will practise deception, and speak impiety against God; He will take away the food of the hungry, And deprive the thirsty of drink.
7 Matakan mazambaci mugaye ne, yana ƙulla mugayen shirye-shirye don yă hallaka talakawa da ƙarairayi, ko sa’ad da roƙon mai bukata da gaskiya ne.
The instruments also of the niggard are evil; He plotteth mischievous devices, To destroy the poor with lying words, Even when the cause of the needy is just.
8 Amma mutumin kirki kan yi shirye-shirye masu kirki, kuma yakan tsaya a kan ayyukan kirki.
But the liberal deviseth liberal things, And in liberal things will he persevere.
9 Ku matan da kuke zaman jin daɗi, ku tashi ku saurare ni; ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya, ku ji abin da zan faɗa!
Arise, hear my voice, ye women that are at ease! Give ear to my speech, ye careless daughters!
10 Cikin ɗan lokaci ƙasa da shekara guda ku da kuke tsammani kuna da kāriya za ku yi rawar jiki; girbin’ya’yan inabi zai kāsa, girbin’ya’yan itatuwa kuma ba zai zo ba.
One year more, and ye shall tremble, ye careless women! For the vintage shall fail; the harvest shall not come.
11 Ku yi rawar jiki, ku mata masu jin daɗi, ku sha wahala, ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya! Ku tuɓe rigunanku, ku ɗaura tsummoki a kwankwasonku.
Tremble, O ye that are at ease! Be in dismay, ye careless ones! Strip you, make you bare, gird ye sackcloth upon your loins!
12 Ku bugi ƙirjinku don gonaki masu kyau don’ya’yan inabi
They shall smite themselves on their breasts, On account of the pleasant fields, On account of the fruitful vine.
13 da kuma don ƙasar mutanena, da ƙasar da ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suka yi girma, I, ku yi kuka saboda dukan gidajen da dā ake biki da kuma domin wannan birnin da dā ake murna a ciki.
Upon the land of my people shall come up thorns and briers; Yea, upon all the houses of joy in the joyous city.
14 Za a ƙyale kagarar, a gudu a bar birnin da dā ake hayaniya; mafaka da hasumiyar tsaro za su zama kango har abada, jin daɗin jakuna, makiyaya don garkuna,
For the palace shall be forsaken; The tumult of the city shall be solitary; The fortified hill and the tower shall be dens forever; The joy of wild-asses, the pasture of flocks;
15 sai an zubo Ruhu a kanmu daga sama, hamada kuma ta zama ƙasar mai taƙi, gona mai taƙi kuma ta zama kamar kurmi.
Until the spirit from on high be poured upon us, And the wilderness become a fruitful field, And the fruitful field be esteemed a forest.
16 Aikin gaskiya zai zauna a hamada adalci kuma zai zauna a ƙasa mai taƙi.
Then shall justice dwell in the wilderness, And righteousness in the fruitful field.
17 Aikin adalci zai zama salama; tasirin adalci zai zama natsuwa da tabbaci har abada.
And the effect of righteousness shall be peace, And the fruit of righteousness quiet and security forever.
18 Mutanena za su zauna lafiya a wuraren salama, a gidaje masu kāriya, a wuraren hutun da babu fitina.
Then shall my people dwell in peaceful habitations, In secure dwellings, in quiet resting-places.
19 Ko da yake ƙanƙara za tă fāɗo a jeji, a kuma rurrushe birni gaba ɗaya,
But the hail shall descend, and the forest shall fall; And the city shall be brought very low.
20 zai zama muku da albarka, ku da kuke shuki iri kusa da kowane rafi, kuna kuma barin lafiyayyiyar makiyaya domin shanu da jakunanku.
Happy ye who sow beside all waters; Who send forth thither the feet of the ox and the ass!

< Ishaya 32 >