< Ishaya 31 >

1 Kaiton waɗanda suka gangara zuwa Masar don neman taimako, waɗanda suke dogara ga dawakai, waɗanda suke dogara ga yawan kekunan yaƙinsu da kuma a girman ƙarfin mahayan dawakansu, amma ba sa dogara ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila, ko ya nemi taimako daga Ubangiji.
Ve dem som farer ned til Egypten efter hjelp og setter sin lit til hester og stoler på vogner fordi de er mange, og på hestfolk fordi de er så tallrike, men ikke vender sine øine til Israels Hellige og ikke søker Herren!
2 Shi ma yana da hikima kuma zai iya kawo masifa; ba ya janye kalmominsa. Zai yi gāba da gidan mugu, gāba da waɗanda suke taimakon masu aikata mugunta.
Men også han er vis, han lar ulykke komme, og sine ord tar han ikke tilbake; men han reiser sig mot de ondes hus og mot deres hjelp som gjør urett.
3 Amma Masarawa mutane ne ba Allah ba; dawakansu nama da jini ne ba ruhu ba. Sa’ad da Ubangiji ya miƙa hannunsa, shi da yake taimako zai yi tuntuɓe shi da aka taimaka zai fāɗi; dukansu biyu za su hallaka tare.
Og egypterne er mennesker og ikke Gud, og deres hester er kjøtt og ikke ånd, og Herren skal rekke ut sin hånd, og hjelperen skal snuble, og den hjulpne falle, og de skal omkomme alle sammen.
4 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Kamar yadda zaki kan yi ruri babban zaki a kan abin da ya yi farauta, kuma ko da yake dukan ƙungiyar makiyaya sun taru wuri ɗaya a kansa, ba zai jijjigu ta wurin ihunsu ba ko ya damu da kiraye-kirayensu, ta haka Ubangiji Maɗaukaki zai sauko don yă yi yaƙi a kan Dutsen Sihiyona da kuma a kan ƙwanƙolinsa.
For så sa Herren til mig: Likesom en løve, en ungløve, knurrer over sitt rov, om en hel flokk hyrder kalles sammen mot den, og ikke skremmes av deres skrik og ikke blir redd for den støi de gjør, således skal Herren, hærskarenes Gud, fare ned for å stride mot Sions berg og mot Jerusalem-haugen.
5 Kamar tsuntsaye masu shawagi a sama haka Ubangiji Maɗaukaki zai kiyaye Urushalima; zai kāre ta ya kuma fanshe ta, zai ‘ƙetare’ ta ya kuma kuɓutar da ita.”
Som fuglene breder ut sine vinger, således skal Herren, hærskarenes Gud, verne Jerusalem, verne og frelse, gå forbi og redde.
6 Ku dawo gare shi ku da kuka yi masa babban tayarwa, ya Isra’ilawa.
Vend om til ham som I er falt fra så dypt, I Israels barn!
7 Gama a wannan rana kowannenku zai ƙi gumakan azurfa da zinariya da hannuwanku masu zunubi suka yi.
For på den tid skal hver av eder forkaste sine sølvguder og gullguder, som eders hender har gjort eder til å synde med.
8 “Za a karkashe Assuriyawa da takobin da ba na yin mutum ba; takobi, da ba na yin mutum ba, zai cinye. Za su gudu daga takobi za a kuma sa samarinsu aikin dole.
Og Assur skal falle for et sverd som ikke er en manns, og et sverd som ikke er et menneskes, skal fortære ham, og han skal rømme for sverdet, og hans unge menn skal bli træler.
9 Kagararsu za tă fāɗi saboda razana; da ganin matsayin yaƙin, shugabannin yaƙinsu za su firgita,” in ji Ubangiji, wanda wutarsa tana a Sihiyona, wanda matoyarsa tana a Urushalima.
Og hans klippe skal rømme i redsel, og hans fyrster skal skremmes bort fra sitt banner, sier Herren, han som har sin ild i Sion og sin ovn i Jerusalem.

< Ishaya 31 >