< Ishaya 31 >

1 Kaiton waɗanda suka gangara zuwa Masar don neman taimako, waɗanda suke dogara ga dawakai, waɗanda suke dogara ga yawan kekunan yaƙinsu da kuma a girman ƙarfin mahayan dawakansu, amma ba sa dogara ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila, ko ya nemi taimako daga Ubangiji.
Ak vai, tiem, kas uz Ēģipti iet pēc palīdzības un paļaujas uz zirgiem un cerē uz ratiem, tāpēc ka to ir daudz, un uz jātniekiem, tāpēc ka to ir liels pulks, bet uz to Svēto iekš Israēla nerauga un To Kungu nemeklē.
2 Shi ma yana da hikima kuma zai iya kawo masifa; ba ya janye kalmominsa. Zai yi gāba da gidan mugu, gāba da waɗanda suke taimakon masu aikata mugunta.
Bet arī Viņš ir gudrs un liek ļaunumam nākt un neņem atpakaļ Savus vārdus, bet ceļas pret bezdievīgo namu un pret ļauna darītāju palīgu.
3 Amma Masarawa mutane ne ba Allah ba; dawakansu nama da jini ne ba ruhu ba. Sa’ad da Ubangiji ya miƙa hannunsa, shi da yake taimako zai yi tuntuɓe shi da aka taimaka zai fāɗi; dukansu biyu za su hallaka tare.
Jo ēģiptieši ir cilvēki un ne Dievs, un viņu zirgi ir miesa un ne gars. Un Tas Kungs izstieps Savu roku, un tas palīgs klūp un, kam top līdzēts, tas krīt, un tie visi kopā iet bojā.
4 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Kamar yadda zaki kan yi ruri babban zaki a kan abin da ya yi farauta, kuma ko da yake dukan ƙungiyar makiyaya sun taru wuri ɗaya a kansa, ba zai jijjigu ta wurin ihunsu ba ko ya damu da kiraye-kirayensu, ta haka Ubangiji Maɗaukaki zai sauko don yă yi yaƙi a kan Dutsen Sihiyona da kuma a kan ƙwanƙolinsa.
Jo tā Tas Kungs uz mani sacījis: tā kā lauva un kā jauns lauva rūc par savu laupījumu, un, jebšu pret viņu liels ganu pulks top sasaukts, tomēr viņš neizbīstas priekš viņu balss un nebaidās no viņa lielā pulka, tāpat Tas Kungs Cebaot nolaidīsies, karot uz Ciānas kalna un uz viņas augstuma.
5 Kamar tsuntsaye masu shawagi a sama haka Ubangiji Maɗaukaki zai kiyaye Urushalima; zai kāre ta ya kuma fanshe ta, zai ‘ƙetare’ ta ya kuma kuɓutar da ita.”
Tā kā putni lidinājās, tāpat Tas Kungs Cebaot apklās Jeruzālemi, un apklādams izpestīs un žēlodams izglābs.
6 Ku dawo gare shi ku da kuka yi masa babban tayarwa, ya Isra’ilawa.
Atgriežaties, Israēla bērni, pie Tā, no kā tik tālu esat atkāpušies.
7 Gama a wannan rana kowannenku zai ƙi gumakan azurfa da zinariya da hannuwanku masu zunubi suka yi.
Jo tai dienā tie atmetīs ikkatrs savus sudraba elkus un savus zelta elkus, ko jūsu rokas ir taisījušas sev par grēku.
8 “Za a karkashe Assuriyawa da takobin da ba na yin mutum ba; takobi, da ba na yin mutum ba, zai cinye. Za su gudu daga takobi za a kuma sa samarinsu aikin dole.
Un Asurs kritīs caur zobenu, bet ne caur vīra zobenu, un to norīs, bet ne cilvēka zobens, un tas bēgs no zobena un viņa jaunekļi paliks par vergiem.
9 Kagararsu za tă fāɗi saboda razana; da ganin matsayin yaƙin, shugabannin yaƙinsu za su firgita,” in ji Ubangiji, wanda wutarsa tana a Sihiyona, wanda matoyarsa tana a Urushalima.
Un viņa kalns trīcēs no bailēm, un viņa lielkungi iztrūcināti bēgs no karoga; to saka Tas Kungs, kam Ciānā uguns un Jeruzālemē ugunskurs.

< Ishaya 31 >