< Ishaya 31 >
1 Kaiton waɗanda suka gangara zuwa Masar don neman taimako, waɗanda suke dogara ga dawakai, waɗanda suke dogara ga yawan kekunan yaƙinsu da kuma a girman ƙarfin mahayan dawakansu, amma ba sa dogara ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila, ko ya nemi taimako daga Ubangiji.
Wo to hem that goon doun in to Egipt to help, and hopen in horsis, and han trist on cartis, for tho ben manye, and on knyytis, for thei ben ful stronge; and thei tristiden not on the hooli of Israel, and thei souyten not the Lord.
2 Shi ma yana da hikima kuma zai iya kawo masifa; ba ya janye kalmominsa. Zai yi gāba da gidan mugu, gāba da waɗanda suke taimakon masu aikata mugunta.
Forsothe he that is wijs, hath brouyt yuel, and took not awei hise wordis; and he schal rise togidere ayens the hous of worste men, and ayens the helpe of hem that worchen wickidnesse.
3 Amma Masarawa mutane ne ba Allah ba; dawakansu nama da jini ne ba ruhu ba. Sa’ad da Ubangiji ya miƙa hannunsa, shi da yake taimako zai yi tuntuɓe shi da aka taimaka zai fāɗi; dukansu biyu za su hallaka tare.
Egipt is a man, and not God; and the horsis of hem ben fleisch, and not spirit; and the Lord schal bowe doun his hond, and the helpere schal falle doun, and he schal falle, to whom help is youun, and alle schulen be wastid togidere.
4 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Kamar yadda zaki kan yi ruri babban zaki a kan abin da ya yi farauta, kuma ko da yake dukan ƙungiyar makiyaya sun taru wuri ɗaya a kansa, ba zai jijjigu ta wurin ihunsu ba ko ya damu da kiraye-kirayensu, ta haka Ubangiji Maɗaukaki zai sauko don yă yi yaƙi a kan Dutsen Sihiyona da kuma a kan ƙwanƙolinsa.
For whi the Lord seith these thingis to me, If a lioun rorith, and a whelp of a lioun on his prey, whanne the multitude of schipherdis cometh ayens hym, he schal not drede of the vois of hem, and he schal not drede of the multitude of hem; so the Lord of oostis schal come doun, for to fiyte on the mounteyn of Sion, and on the litil hil therof.
5 Kamar tsuntsaye masu shawagi a sama haka Ubangiji Maɗaukaki zai kiyaye Urushalima; zai kāre ta ya kuma fanshe ta, zai ‘ƙetare’ ta ya kuma kuɓutar da ita.”
As briddis fleynge, so the Lord of oostis schal defende Jerusalem; he defendynge and delyuerynge, passynge forth and sauynge.
6 Ku dawo gare shi ku da kuka yi masa babban tayarwa, ya Isra’ilawa.
Ye sones of Israel, be conuertid, as ye hadden go awei in to depthe.
7 Gama a wannan rana kowannenku zai ƙi gumakan azurfa da zinariya da hannuwanku masu zunubi suka yi.
Forsothe in that dai a man schal caste awei the idols of his siluer, and the idols of his gold, whiche youre hondis maden to you in to synne.
8 “Za a karkashe Assuriyawa da takobin da ba na yin mutum ba; takobi, da ba na yin mutum ba, zai cinye. Za su gudu daga takobi za a kuma sa samarinsu aikin dole.
And Assur schal falle bi swerd, not of man, and a swerd, not of man, schal deuoure hym; and he schal fle, not fro the face of swerd, and hise yonge men schulen be tributaries;
9 Kagararsu za tă fāɗi saboda razana; da ganin matsayin yaƙin, shugabannin yaƙinsu za su firgita,” in ji Ubangiji, wanda wutarsa tana a Sihiyona, wanda matoyarsa tana a Urushalima.
and the strengthe of hym schal passe fro ferdfulnesse, and hise princes fleynge schulen drede. The Lord seide, whos fier is in Sion, and his chymeney is in Jerusalem.