< Ishaya 31 >

1 Kaiton waɗanda suka gangara zuwa Masar don neman taimako, waɗanda suke dogara ga dawakai, waɗanda suke dogara ga yawan kekunan yaƙinsu da kuma a girman ƙarfin mahayan dawakansu, amma ba sa dogara ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila, ko ya nemi taimako daga Ubangiji.
Terrible things will happen to those who reply on Egypt to help them, trusting in their soldiers’ horses and their many chariots and their strong chariot-drivers, instead of trusting that Yahweh, the Holy One of Israel, will help them.
2 Shi ma yana da hikima kuma zai iya kawo masifa; ba ya janye kalmominsa. Zai yi gāba da gidan mugu, gāba da waɗanda suke taimakon masu aikata mugunta.
Yahweh is [very] wise, [but] he also causes people to experience disaster! And [when he decides to do that], he does not change his mind! He will strike/punish the wicked people and [all] those who help them.
3 Amma Masarawa mutane ne ba Allah ba; dawakansu nama da jini ne ba ruhu ba. Sa’ad da Ubangiji ya miƙa hannunsa, shi da yake taimako zai yi tuntuɓe shi da aka taimaka zai fāɗi; dukansu biyu za su hallaka tare.
The soldiers of Egypt [that you people of Judah are relying on] are humans, not God! And their horses are only horses; they are not [powerful] spirits! So when Yahweh raises his fist to strike/punish the [soldiers of Egypt whom you thought would help you], he will also strike [you who thought that you would be helped], and you and they will stumble and fall down; all of you will die together.
4 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Kamar yadda zaki kan yi ruri babban zaki a kan abin da ya yi farauta, kuma ko da yake dukan ƙungiyar makiyaya sun taru wuri ɗaya a kansa, ba zai jijjigu ta wurin ihunsu ba ko ya damu da kiraye-kirayensu, ta haka Ubangiji Maɗaukaki zai sauko don yă yi yaƙi a kan Dutsen Sihiyona da kuma a kan ƙwanƙolinsa.
But this is what Yahweh said to me: “When a huge lion stands over the body of a sheep that he has killed and growls, even if a large group of shepherds comes [to chase/shoo away the lion], even if they shout loudly, the lion will not be afraid and will not leave. Similarly, I, the Commander of the armies of angels, will come down to fight [my enemies] on Zion Hill, [and nothing will hinder me].
5 Kamar tsuntsaye masu shawagi a sama haka Ubangiji Maɗaukaki zai kiyaye Urushalima; zai kāre ta ya kuma fanshe ta, zai ‘ƙetare’ ta ya kuma kuɓutar da ita.”
[I], the Commander of the armies of angels, will protect Jerusalem like [SIM] a [mother] bird protects [the baby birds in] her nest: I will defend the city and rescue it from its enemies.”
6 Ku dawo gare shi ku da kuka yi masa babban tayarwa, ya Isra’ilawa.
My people, [even though] you have greatly rebelled against Yahweh, return to him.
7 Gama a wannan rana kowannenku zai ƙi gumakan azurfa da zinariya da hannuwanku masu zunubi suka yi.
When you do that, each of you will throw away the idols that you [SYN] have sinned by making, idols that are [covered with] silver and gold.
8 “Za a karkashe Assuriyawa da takobin da ba na yin mutum ba; takobi, da ba na yin mutum ba, zai cinye. Za su gudu daga takobi za a kuma sa samarinsu aikin dole.
[Many of the] Assyrian [soldiers] will be killed, but not by swords that men use. They will be destroyed by the sword of God; and [those who are not killed] will (panic/be very afraid) and flee. And some of them will [be captured] and forced to become slaves.
9 Kagararsu za tă fāɗi saboda razana; da ganin matsayin yaƙin, shugabannin yaƙinsu za su firgita,” in ji Ubangiji, wanda wutarsa tana a Sihiyona, wanda matoyarsa tana a Urushalima.
[Even] their very strong soldiers [MTY] will be terrified; they will abandon their battle flags and run away! Yahweh will cause his enemies who attack Jerusalem to be destroyed. Yahweh’s presence on Zion Hill is [like] a fire, [like] a furnace that blazes in Jerusalem; and that is what Yahweh says [about what will happen to the Assyrian army]!

< Ishaya 31 >