< Ishaya 31 >

1 Kaiton waɗanda suka gangara zuwa Masar don neman taimako, waɗanda suke dogara ga dawakai, waɗanda suke dogara ga yawan kekunan yaƙinsu da kuma a girman ƙarfin mahayan dawakansu, amma ba sa dogara ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila, ko ya nemi taimako daga Ubangiji.
Woe to them that go down to Egypt for help, and stay on horses; and trust in chariots, because they are many, and in horsemen, because they are very strong; but they look not unto the Holy One of Israel, neither seek the LORD!
2 Shi ma yana da hikima kuma zai iya kawo masifa; ba ya janye kalmominsa. Zai yi gāba da gidan mugu, gāba da waɗanda suke taimakon masu aikata mugunta.
Yet he also is wise, and will bring evil, and will not call back his words: but will arise against the house of the evil-doers, and against the help of them that work iniquity.
3 Amma Masarawa mutane ne ba Allah ba; dawakansu nama da jini ne ba ruhu ba. Sa’ad da Ubangiji ya miƙa hannunsa, shi da yake taimako zai yi tuntuɓe shi da aka taimaka zai fāɗi; dukansu biyu za su hallaka tare.
Now the Egyptians are men, and not God; and their horses flesh, and not spirit: and when the LORD shall stretch out his hand, both he that helpeth shall stumble, and he that is holpen shall fall, and they all shall fail together.
4 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Kamar yadda zaki kan yi ruri babban zaki a kan abin da ya yi farauta, kuma ko da yake dukan ƙungiyar makiyaya sun taru wuri ɗaya a kansa, ba zai jijjigu ta wurin ihunsu ba ko ya damu da kiraye-kirayensu, ta haka Ubangiji Maɗaukaki zai sauko don yă yi yaƙi a kan Dutsen Sihiyona da kuma a kan ƙwanƙolinsa.
For thus saith the LORD unto me, Like as when the lion growleth and the young lion over his prey, if a multitude of shepherds be called forth against him, he will not be dismayed at their voice, nor abase himself for the noise of them: so shall the LORD of hosts come down to fight upon mount Zion, and upon the hill thereof.
5 Kamar tsuntsaye masu shawagi a sama haka Ubangiji Maɗaukaki zai kiyaye Urushalima; zai kāre ta ya kuma fanshe ta, zai ‘ƙetare’ ta ya kuma kuɓutar da ita.”
As birds flying, so will the LORD of hosts protect Jerusalem; he will protect and deliver [it], he will pass over and preserve [it].
6 Ku dawo gare shi ku da kuka yi masa babban tayarwa, ya Isra’ilawa.
Turn ye unto him from whom ye have deeply revolted, O children of Israel.
7 Gama a wannan rana kowannenku zai ƙi gumakan azurfa da zinariya da hannuwanku masu zunubi suka yi.
For in that day they shall cast away every man his idols of silver, and his idols of gold, which your own hands have made unto you for a sin.
8 “Za a karkashe Assuriyawa da takobin da ba na yin mutum ba; takobi, da ba na yin mutum ba, zai cinye. Za su gudu daga takobi za a kuma sa samarinsu aikin dole.
Then shall the Assyrian fall with the sword, not of man; and the sword, not of men, shall devour him: and he shall flee from the sword, and his young men shall become tributary.
9 Kagararsu za tă fāɗi saboda razana; da ganin matsayin yaƙin, shugabannin yaƙinsu za su firgita,” in ji Ubangiji, wanda wutarsa tana a Sihiyona, wanda matoyarsa tana a Urushalima.
And his rock shall pass away by reason of terror, and his princes shall be dismayed at the ensign, saith the LORD, whose fire is in Zion, and his furnace in Jerusalem.

< Ishaya 31 >