< Ishaya 31 >

1 Kaiton waɗanda suka gangara zuwa Masar don neman taimako, waɗanda suke dogara ga dawakai, waɗanda suke dogara ga yawan kekunan yaƙinsu da kuma a girman ƙarfin mahayan dawakansu, amma ba sa dogara ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila, ko ya nemi taimako daga Ubangiji.
Woe to those who descend into Egypt for assistance, hoping in horses, and putting their trust in four-horse chariots because they are many, and in horsemen because they are exceedingly strong. And they have not believed in the Holy One of Israel, and they have not sought the Lord.
2 Shi ma yana da hikima kuma zai iya kawo masifa; ba ya janye kalmominsa. Zai yi gāba da gidan mugu, gāba da waɗanda suke taimakon masu aikata mugunta.
Therefore, being wise, he has permitted harm, and he has not removed his words, and he will rise up against the house of the wicked and against those who assist the workers of iniquity.
3 Amma Masarawa mutane ne ba Allah ba; dawakansu nama da jini ne ba ruhu ba. Sa’ad da Ubangiji ya miƙa hannunsa, shi da yake taimako zai yi tuntuɓe shi da aka taimaka zai fāɗi; dukansu biyu za su hallaka tare.
Egypt is man, and not God. And their horses are flesh, and not spirit. And so, the Lord will reach down his hand, and the helper will fall, and the one who was being helped will fall, and they will all be consumed together.
4 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Kamar yadda zaki kan yi ruri babban zaki a kan abin da ya yi farauta, kuma ko da yake dukan ƙungiyar makiyaya sun taru wuri ɗaya a kansa, ba zai jijjigu ta wurin ihunsu ba ko ya damu da kiraye-kirayensu, ta haka Ubangiji Maɗaukaki zai sauko don yă yi yaƙi a kan Dutsen Sihiyona da kuma a kan ƙwanƙolinsa.
For the Lord says this to me: In the same way that a lion roars, and a young lion is over his prey, and though a multitude of shepherds may meet him, he will not dread their voice, nor be afraid of their number, so will the Lord of hosts descend in order to battle upon mount Zion and upon its hill.
5 Kamar tsuntsaye masu shawagi a sama haka Ubangiji Maɗaukaki zai kiyaye Urushalima; zai kāre ta ya kuma fanshe ta, zai ‘ƙetare’ ta ya kuma kuɓutar da ita.”
Like birds flying, so will the Lord of hosts protect Jerusalem, protecting and freeing, passing over and saving.
6 Ku dawo gare shi ku da kuka yi masa babban tayarwa, ya Isra’ilawa.
Be converted to the same depth that you have drawn away, O sons of Israel.
7 Gama a wannan rana kowannenku zai ƙi gumakan azurfa da zinariya da hannuwanku masu zunubi suka yi.
For in that day, a man will cast away his idols of silver and his idols of gold, which your hands have made for you unto sin.
8 “Za a karkashe Assuriyawa da takobin da ba na yin mutum ba; takobi, da ba na yin mutum ba, zai cinye. Za su gudu daga takobi za a kuma sa samarinsu aikin dole.
And Assur will fall by a sword not of man, and a sword not of man will devour him. And he will not flee from the face of the sword, and his young men will be subject to a penalty.
9 Kagararsu za tă fāɗi saboda razana; da ganin matsayin yaƙin, shugabannin yaƙinsu za su firgita,” in ji Ubangiji, wanda wutarsa tana a Sihiyona, wanda matoyarsa tana a Urushalima.
And his strength will pass away in terror, and his princes will flee in fear. The Lord has said it. His fire is in Zion, and his furnace is at Jerusalem.

< Ishaya 31 >