< Ishaya 30 >

1 “Kaiton’ya’ya masu tayarwa,” in ji Ubangiji, “ga waɗanda suke ƙulle-ƙullen da ba nawa ba, suna yin yarjejjeniya, amma ba ta Ruhuna ba, suna jibga zunubi a kan zunubi;
“Ai das crianças rebeldes”, diz Javé, “que tomam conselho, mas não de mim; e que fazem uma aliança, mas não com meu Espírito, para acrescentar pecado ao pecado;
2 waɗanda suka gangara zuwa Masar ba tare da sun nemi shawarata; waɗanda suke neman taimakon kāriyar Fir’auna, don neman inuwar mafakar Masar.
que se propôs a descer ao Egito sem pedir meu conselho, a se fortalecer na força do Faraó, e a se refugiar na sombra do Egito!
3 Amma kāriyar Fir’auna za tă zama muku abin kunya, inuwar Masar za tă jawo muku kunya.
Portanto, a força do Faraó será sua vergonha, e o refúgio à sombra do Egito, sua confusão.
4 Ko da yake suna da shugabanni a Zowan kuma jakadunsu sun iso Hanes,
Pois seus príncipes estão em Zoan, e seus embaixadores vieram a Hanes.
5 kowa zai sha kunya saboda mutanen da ba su da amfani gare su, waɗanda ba sa taimako ko amfani, sai dai jawo kunya da da-na-sani.”
Todos eles terão vergonha por causa de um povo que não pode lucrar com eles, que não são uma ajuda nem um lucro, mas uma vergonha e também uma reprovação”.
6 Allah ya faɗa game da dabbobin Negeb cewa, Ta cikin ƙasa mai wahala da mai hatsari inda zakoki da zakanya, inda macizai masu dafi da macizai masu tashi sama suke, jakadu na ɗaukan arzikinsu a kan jakuna, dukiyarsu a kan raƙuma, zuwa ƙasan nan marar riba,
O fardo dos animais do Sul. Através da terra de problemas e angústias, da leoa e do leão, da víbora e da serpente voadora ardente, eles carregam suas riquezas sobre os ombros de burros jovens, e seus tesouros sobre as lombadas de camelos, para um povo não lucrativo.
7 zuwa Masar, wadda taimakonta marar amfani ne. Saboda haka na yi mata laƙabi Rahab Marar Yin Kome.
Pois o Egito ajuda em vão, e sem nenhum propósito; por isso a chamei de Rahab que fica quieta.
8 Tafi yanzu, ka rubuta musu a kan allo, ka rubuta shi a kan littafi, cewa kwanaki suna zuwa zai zama madawwamin shaida.
Agora vá, escreva-o diante deles em uma tábua, e inscreva-o em um livro, para que possa ser para sempre e eternamente.
9 Waɗannan mutane masu tawaye,’ya’ya masu ruɗu,’ya’yan da ba sa niyya su saurara ga umarnan Ubangiji.
Pois é um povo rebelde, crianças mentirosas, crianças que não ouvirão a lei de Javé;
10 Sukan ce wa masu gani, “Kada ku ƙara ganin wahayi!” Ga annabawa kuwa sukan ce, “Kada ku ƙara ba mu wahayin abin da yake daidai! Faɗa mana abubuwan da muke so mu ji ne kawai, ku yi annabcin abin da zai ruɗe mu.
que dizem aos videntes: “Não vejam!” e aos profetas: “Não nos profetizem coisas corretas”. Diga-nos coisas agradáveis. Profetizem enganos.
11 Ku bar wannan hanya, ku tashi daga wannan hanya, ku kuma daina kalubalantarmu da Mai Tsarkin nan na Isra’ila!”
Saiam do caminho. Saiam do caminho. Porque o Santo de Israel deve cessar de nos preceder”.
12 Saboda haka, ga abin da Mai Tsarkin nan na Isra’ila yake cewa, “Saboda haka kun ƙi wannan saƙo, kuka dogara ga aikin kama-karya kuka kuma dogara ga yin ruɗu,
Portanto, o Santo de Israel diz: “Porque você despreza esta palavra, e confia na opressão e perversidade, e confia nela,
13 wannan zunubi zai zama muku kamar bango mai tsayi, tsagagge da yake kuma fāɗuwa, da zai rushe nan da nan, ba tsammani.
portanto esta iniquidade será para você como uma brecha pronta para cair, inchando em um muro alto, cuja quebra vem repentinamente em um instante.
14 Zai rushe kucu-kucu kamar tukunyar yumɓu, ya ragargaje ƙaf har cikin gutsattsarinsa ba za a sami ko ɗan katanga don ɗiba garwashin wuta ko a ɗiba ruwa daga tanki ba.”
Ele a quebrará como se quebra um vaso de oleiro, quebrando-o em pedaços sem poupar, para que não se encontre entre os pedaços quebrados um pedaço suficientemente bom para tirar o fogo da lareira, ou para mergulhar água da cisterna”.
15 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya faɗa, “Cikin tuba da hutu ne kaɗai cetonku yake, cikin shiru da dogara gare ni ne za ku sami ƙarfinku, amma ba za ku sami ko ɗaya a cikinsu ba.
Pois assim disse o Senhor Javé, o Santo de Israel: “Você será salvo ao voltar e descansar”. Vossa força estará em silêncio e em confiança”. Você recusou,
16 Kun ce, ‘A’a, za mu gudu a kan dawakai.’ Saboda haka za ku gudu! Kun ce, ‘Za mu hau dawakai masu sauri mu gudu.’ Saboda haka masu fafararku za su fi ku gudu!
mas disse: “Não, pois fugiremos a cavalo;” portanto você fugirá; e, “cavalgaremos no veloz;” portanto aqueles que o perseguem serão velozes.
17 Dubu za su gudu don barazanar mutum guda; da jin barazanar mutane biyar dukanku za ku yi ta gudu sai an bar ku kamar sandar tuta a kan dutse, kamar tuta a kan tudu.”
Mil fugirão com a ameaça de um. Com a ameaça de cinco, vocês fugirão até ficarem como um farol no topo de uma montanha, e como um estandarte em uma colina.
18 Duk da haka Ubangiji yana marmari ya yi muku alheri; ya tashi don yă nuna muku jinƙai. Gama Ubangiji Allah ne mai aikata gaskiya. Masu albarka ne dukanku waɗanda suke dogara gare shi!
Portanto Yahweh esperará, para que seja gracioso para convosco; e por isso será exaltado, para que tenha misericórdia de vós, pois Yahweh é um Deus de justiça. Abençoados sejam todos aqueles que esperam por ele.
19 Ya mutanen Sihiyona, waɗanda suke zama a Urushalima, ba za ku ƙara kuka ba. Zai zama mai alheri sa’ad da kuka yi kukan neman taimako! Da zarar ya ji, zai amsa muku.
Pois o povo habitará em Sião, em Jerusalém. Não choreis mais. Ele certamente será gracioso convosco à voz de vosso grito. Quando ele vos ouvir, ele vos responderá.
20 Ko da yake Ubangiji yakan ba da abincin azaba da ruwan wahala, ba za a ƙara ɓoye malamanku ba; da idanunku za ku gan su.
Though o Senhor pode lhe dar o pão da adversidade e a água da aflição, mas seus professores não mais se esconderão, mas seus olhos verão seus professores;
21 Ko kun juye dama ko hagu, kunnuwanku za su ji murya a bayanku tana cewa, “Ga hanya; ku yi tafiya a kai.”
e quando você se vira para a direita, e quando você se vira para a esquerda, seus ouvidos ouvirão uma voz atrás de você, dizendo: “Este é o caminho”. Caminhe por ela”.
22 Sa’an nan za ku ƙazantar da gumakanku da kuka dalaye da zinariya; za ku zubar da su kamar rigar al’adar mace ku kuma ce musu, “Ku ɓace mana da gani!”
Você profanará a sobreposição de suas imagens gravadas de prata, e o revestimento de suas imagens fundidas de ouro. Você as jogará fora como uma coisa impura. Você dirá: “Vá embora!”.
23 Zai kuma aiko muku da ruwan sama don shuki a ƙasa, kuma abincin da zai fito daga gona zai zama mai albarka da kuma mai yawa. A wannan rana shanu za su yi kiwo a wadatacciyar makiyaya.
Ele dará a chuva para sua semente, com a qual você semeará a terra; e o pão do aumento da terra será rico e abundante. Naquele dia, seu gado se alimentará em grandes pastagens.
24 Shanunku da jakunanku da suke huɗar gonakinku za su ci harawa mafi kyau, wanda an sheƙe shi da babban cokali mai yatsu da kuma babban cokali.
Os bois também e os burros jovens que até o solo comerão ração saborosa, que foi limpa com a pá e com o garfo.
25 A ranar babban kisa, sa’ad da hasumiyoyi za su fāɗi, rafuffukan ruwa za su malalo a kan kowane dutse da kowane tudu mai tsawo.
Haverá riachos e riachos de água em cada montanha alta e em cada colina alta no dia do grande massacre, quando as torres caírem.
26 Wata zai yi haske kamar rana, kuma hasken rana zai ma yi sau bakwai na haskenta, kamar hasken cikakku ranaku bakwai, sa’ad da Ubangiji zai ɗaura raunukan mutanensa ya kuma warkar da raunukan da ya yi musu.
Além disso, a luz da lua será como a luz do sol, e a luz do sol será sete vezes mais brilhante, como a luz de sete dias, no dia em que Yahweh ligar a fratura de seu povo, e curar a ferida com que foram atingidos.
27 Duba, Sunan Ubangiji yana zuwa daga nesa, tare da fushi mai ƙuna da kuma baƙin hayaƙi; leɓunansa sun cika da fushi, harshensa kuma wuta ce mai cinyewa.
Eis que o nome de Yahweh vem de longe, queimando com sua raiva, e em espessa fumaça crescente. Seus lábios estão cheios de indignação. Sua língua é como um fogo devorador.
28 Numfashinsa kamar raƙuman ruwa masu gudu yana tashi har zuwa wuya. Yakan tankaɗe al’ummai cikin lariyar hallaka; yakan sa a muƙamuƙan mutane linzamin da zai jagorance su su kauce.
Sua respiração é como uma corrente transbordante que chega até o pescoço, para peneirar as nações com a peneira de destruição. Uma cabeçada que leva à ruína estará nas mandíbulas dos povos.
29 Za ku kuma rera kamar a daren da kuke shagalin biki mai tsarki; zukatanku za su yi farin ciki kamar sa’ad da mutane sukan haura da busa zuwa dutsen Ubangiji, zuwa Dutse na Isra’ila.
Você terá uma canção, como na noite em que se celebra uma festa santa, e alegria de coração, como quando se vai com uma flauta para chegar à montanha de Yahweh, ao Rochedo de Israel.
30 Ubangiji zai sa mutane su ji muryarsa mai daraja ya kuma sa su ga hannunsa na saukowa tare da fushi mai ƙuna da kuma wuta mai cinyewa, gizagizai za su ɓarke, za a yi hadarin tsawa da ƙanƙara.
Javé fará ouvir sua gloriosa voz, e mostrará a descida de seu braço, com a indignação de sua raiva e a chama de um fogo devorador, com uma rajada, tempestade e granizo.
31 Muryar Ubangiji za tă firgita Assuriya da sandar mulkinsa zai kashe su.
Pois através da voz de Iavé, o assírio ficará consternado. Ele o atacará com sua vara.
32 Kowane bugun da Ubangiji zai yi musu da bulalarsa na hukunci zai zama kiɗi ga ganguna da garaya, yayinda yake yaƙi da su da naushin hannunsa.
Cada golpe da vara de punição, que Yahweh colocará sobre ele, será com o som de tamborins e harpas. Ele lutará com eles em batalhas, brandindo armas.
33 An riga an shirya wurin ƙonawa; an shirya shi saboda sarki. An haƙa ramin wutarsa da zurfi da kuma fāɗi, da isashen wuta da itacen wuta; numfashin Ubangiji, yana kamar kibiritu mai ƙuna, da aka sa masa wuta.
Pois seu lugar ardente já está há muito tempo pronto. Sim, ele está preparado para o rei. Ele fez sua pira profunda e grande com fogo e muita lenha. O hálito de Javé, como um fluxo de enxofre, acalma-o.

< Ishaya 30 >