< Ishaya 30 >

1 “Kaiton’ya’ya masu tayarwa,” in ji Ubangiji, “ga waɗanda suke ƙulle-ƙullen da ba nawa ba, suna yin yarjejjeniya, amma ba ta Ruhuna ba, suna jibga zunubi a kan zunubi;
Malheur à vous, fils déserteurs, dit le Seigneur, de ce que vous formez des desseins, et non par moi, et que vous ourdissez une trame, et non par mon esprit, afin d’ajouter péché à péché;
2 waɗanda suka gangara zuwa Masar ba tare da sun nemi shawarata; waɗanda suke neman taimakon kāriyar Fir’auna, don neman inuwar mafakar Masar.
Vous qui marchez pour descendre en Egypte, et n’avez pas interrogé ma bouche, espérant du secours de la force de Pharaon, et ayant confiance dans l’ombre de l’Egypte.
3 Amma kāriyar Fir’auna za tă zama muku abin kunya, inuwar Masar za tă jawo muku kunya.
Et la force de Pharaon vous sera à confusion, et la confiance dans l’ombre de l’Egypte, à ignominie.
4 Ko da yake suna da shugabanni a Zowan kuma jakadunsu sun iso Hanes,
Car tes princes étaient à Tanis, et tes messagers sont parvenus jusqu’à Hanès.
5 kowa zai sha kunya saboda mutanen da ba su da amfani gare su, waɗanda ba sa taimako ko amfani, sai dai jawo kunya da da-na-sani.”
Tous ont été confondus à la vue d’un peuple qui ne pouvait leur être utile; ils ne leur ont pas été à secours et à quelque utilité, mais à confusion et à opprobre.
6 Allah ya faɗa game da dabbobin Negeb cewa, Ta cikin ƙasa mai wahala da mai hatsari inda zakoki da zakanya, inda macizai masu dafi da macizai masu tashi sama suke, jakadu na ɗaukan arzikinsu a kan jakuna, dukiyarsu a kan raƙuma, zuwa ƙasan nan marar riba,
Malheur accablant des bêtes du Midi. Elles vont dans une terre de tribulation et d’angoisse, d’où sortent la lionne et le lion, la vipère et le basilic volant; ils portent sur les épaules des ânes leurs richesses, et sur la bosse des chameaux leurs trésors, à un peuple qui ne pourra pas leur être utile.
7 zuwa Masar, wadda taimakonta marar amfani ne. Saboda haka na yi mata laƙabi Rahab Marar Yin Kome.
Car inutilement et vainement l’Egypte les secourra; voilà pourquoi j’ai crié à ce sujet: C’est de l’orgueil seulement, reste en repos.
8 Tafi yanzu, ka rubuta musu a kan allo, ka rubuta shi a kan littafi, cewa kwanaki suna zuwa zai zama madawwamin shaida.
Maintenant donc entre, écris cela pour lui sur le buis, et dans un livre grave-le soigneusement, et il sera au dernier jour un témoignage à jamais;
9 Waɗannan mutane masu tawaye,’ya’ya masu ruɗu,’ya’yan da ba sa niyya su saurara ga umarnan Ubangiji.
Car c’est un peuple provoquant au courroux, et ce sont des fils menteurs, des fils qui ne veulent pas entendre la loi de Dieu;
10 Sukan ce wa masu gani, “Kada ku ƙara ganin wahayi!” Ga annabawa kuwa sukan ce, “Kada ku ƙara ba mu wahayin abin da yake daidai! Faɗa mana abubuwan da muke so mu ji ne kawai, ku yi annabcin abin da zai ruɗe mu.
Qui disent à ceux qui voient: Ne voyez pas; et à ceux qui regardent: Ne regardez pas pour nous des choses qui sont justes; dites-nous des choses qui nous plaisent, voyez pour nous des erreurs.
11 Ku bar wannan hanya, ku tashi daga wannan hanya, ku kuma daina kalubalantarmu da Mai Tsarkin nan na Isra’ila!”
Eloignez de moi cette voie, détournez de moi ce sentier; qu’il disparaisse de notre face, le saint d’Israël.
12 Saboda haka, ga abin da Mai Tsarkin nan na Isra’ila yake cewa, “Saboda haka kun ƙi wannan saƙo, kuka dogara ga aikin kama-karya kuka kuma dogara ga yin ruɗu,
À cause de cela, voici ce que dit le saint d’Israël: Parce que vous avez rejeté cette parole, et que vous avez espéré dans la calomnie et dans le tumulte, et que vous y avez mis votre appui,
13 wannan zunubi zai zama muku kamar bango mai tsayi, tsagagge da yake kuma fāɗuwa, da zai rushe nan da nan, ba tsammani.
À cause de cela, cette iniquité sera pour vous comme une brèche qui menace ruine, et qui est recherchée dans un mur élevé, parce que tout à coup, tandis qu’on ne s’y attend pas, vient son écroulement.
14 Zai rushe kucu-kucu kamar tukunyar yumɓu, ya ragargaje ƙaf har cikin gutsattsarinsa ba za a sami ko ɗan katanga don ɗiba garwashin wuta ko a ɗiba ruwa daga tanki ba.”
Et elle sera mise en pièces, comme on brise d’un brisement très fort un vase de potier; et on ne trouvera pas parmi ses fragments un têt dans lequel on puisse porter un peu de feu pris d’une incendie, ou puiser un peu d’eau à une fosse,
15 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya faɗa, “Cikin tuba da hutu ne kaɗai cetonku yake, cikin shiru da dogara gare ni ne za ku sami ƙarfinku, amma ba za ku sami ko ɗaya a cikinsu ba.
Parce que voici ce que dit le Seigneur Dieu, le saint d’Israël: Si vous revenez, et vous vous tenez en repos, vous serez sauvés; dans le silence et dans l’espérance sera votre force. Et vous n’avez pas voulu;
16 Kun ce, ‘A’a, za mu gudu a kan dawakai.’ Saboda haka za ku gudu! Kun ce, ‘Za mu hau dawakai masu sauri mu gudu.’ Saboda haka masu fafararku za su fi ku gudu!
Et vous avez dit: Pas du tout; mais nous fuirons vers des chevaux; c’est pour cela que vous fuirez. Et nous monterons sur de rapides coursiers; c’est pour cela que plus rapides seront ceux qui vous poursuivront.
17 Dubu za su gudu don barazanar mutum guda; da jin barazanar mutane biyar dukanku za ku yi ta gudu sai an bar ku kamar sandar tuta a kan dutse, kamar tuta a kan tudu.”
Vous fuirez an nombre de mille hommes par la terreur d’un seul, et tous par la terreur de cinq, jusqu’à ce que vous soyez laissés comme un mât de vaisseau sur une cime de montagne, et comme un étendard sur une colline.
18 Duk da haka Ubangiji yana marmari ya yi muku alheri; ya tashi don yă nuna muku jinƙai. Gama Ubangiji Allah ne mai aikata gaskiya. Masu albarka ne dukanku waɗanda suke dogara gare shi!
À cause de cela, le Seigneur attend, afin d’avoir pitié de vous; et pour cela il sera exalté en vous épargnant; car c’est un Dieu de justice que le Seigneur; bienheureux tous ceux qui l’attendent.
19 Ya mutanen Sihiyona, waɗanda suke zama a Urushalima, ba za ku ƙara kuka ba. Zai zama mai alheri sa’ad da kuka yi kukan neman taimako! Da zarar ya ji, zai amsa muku.
Car le peuple de Sion habitera dans Jérusalem; pleurant tu ne pleureras pas du tout; ayant pitié il aura pitié de toi; à la voix de ton cri, dès qu’il entendra, il te répondra.
20 Ko da yake Ubangiji yakan ba da abincin azaba da ruwan wahala, ba za a ƙara ɓoye malamanku ba; da idanunku za ku gan su.
Et le Seigneur vous donnera un pain restreint et une eau peu abondante; et il ne fera pas que celui qui t’instruit s’en aille loin de toi; et tes yeux verront ton maître.
21 Ko kun juye dama ko hagu, kunnuwanku za su ji murya a bayanku tana cewa, “Ga hanya; ku yi tafiya a kai.”
Et tes oreilles entendront la voix de celui qui, derrière toi, t’avertira: Voici la voie, marchez-y; et ne vous détournez ni à droite ni à gauche,
22 Sa’an nan za ku ƙazantar da gumakanku da kuka dalaye da zinariya; za ku zubar da su kamar rigar al’adar mace ku kuma ce musu, “Ku ɓace mana da gani!”
Et tu regarderas comme choses souillées les lames d’argent de tes images taillées au ciseau, et le vêtement de ta statue d’or jetée en fonte, et tu les rejetteras comme un linge souillé. Sors, lui diras-tu;
23 Zai kuma aiko muku da ruwan sama don shuki a ƙasa, kuma abincin da zai fito daga gona zai zama mai albarka da kuma mai yawa. A wannan rana shanu za su yi kiwo a wadatacciyar makiyaya.
Et la pluie sera accordée à ta semence, partout où tu auras semé sur la terre, et le pain produit des grains de la terre sera très abondant et gras; dans ta possession, en ce jour-là, l’agneau paîtra spacieusement.
24 Shanunku da jakunanku da suke huɗar gonakinku za su ci harawa mafi kyau, wanda an sheƙe shi da babban cokali mai yatsu da kuma babban cokali.
Et les taureaux et les petits des ânes qui labourent la terre, mangeront les grains mêlés ensemble, comme dans l’aire ils auront été vannés.
25 A ranar babban kisa, sa’ad da hasumiyoyi za su fāɗi, rafuffukan ruwa za su malalo a kan kowane dutse da kowane tudu mai tsawo.
Et il y aura sur toute haute montagne et sur toute colline élevée, des ruisseaux d’eaux courantes, au jour où beaucoup auront été tués, et lorsque seront tombées les tours.
26 Wata zai yi haske kamar rana, kuma hasken rana zai ma yi sau bakwai na haskenta, kamar hasken cikakku ranaku bakwai, sa’ad da Ubangiji zai ɗaura raunukan mutanensa ya kuma warkar da raunukan da ya yi musu.
Et sera la lumière de la lune comme la lumière du soleil, et la lumière du soleil sera septuplée, égale à la lumière de sept jours, au jour où le Seigneur aura lié la blessure de son peuple et guéri le coup de sa plaie.
27 Duba, Sunan Ubangiji yana zuwa daga nesa, tare da fushi mai ƙuna da kuma baƙin hayaƙi; leɓunansa sun cika da fushi, harshensa kuma wuta ce mai cinyewa.
Voici que le nom du Seigneur vient de loin; ardente est sa fureur, et lourde à porter; ses lèvres sont pleines d’indignation, sa langue est comme un feu dévorant.
28 Numfashinsa kamar raƙuman ruwa masu gudu yana tashi har zuwa wuya. Yakan tankaɗe al’ummai cikin lariyar hallaka; yakan sa a muƙamuƙan mutane linzamin da zai jagorance su su kauce.
Son souffle est un torrent débordé, qui atteint jusqu’au milieu du cou, pour réduire des nations au néant, et briser le frein d’erreur qui était aux mâchoires des peuples.
29 Za ku kuma rera kamar a daren da kuke shagalin biki mai tsarki; zukatanku za su yi farin ciki kamar sa’ad da mutane sukan haura da busa zuwa dutsen Ubangiji, zuwa Dutse na Isra’ila.
Vous chanterez comme dans la nuit d’une sainte solennité, et la joie de votre cœur sera comme la joie de celui qui va avec la flûte, afin de se présenter sur la montagne du Seigneur, au fort d’Israël.
30 Ubangiji zai sa mutane su ji muryarsa mai daraja ya kuma sa su ga hannunsa na saukowa tare da fushi mai ƙuna da kuma wuta mai cinyewa, gizagizai za su ɓarke, za a yi hadarin tsawa da ƙanƙara.
Et le Seigneur fera entendre la majesté de sa voix, et il montrera la terreur de son bras dans une menace de fureur, et dans la flamme d’un feu dévorant; il brisera par un tourbillon et par des pierres de grêle.
31 Muryar Ubangiji za tă firgita Assuriya da sandar mulkinsa zai kashe su.
Car à la voix du Seigneur Assur tremblera d’effroi, frappé de sa verge.
32 Kowane bugun da Ubangiji zai yi musu da bulalarsa na hukunci zai zama kiɗi ga ganguna da garaya, yayinda yake yaƙi da su da naushin hannunsa.
Et le passage de la verge sera affermi; le Seigneur la fera reposer sur lui au milieu des tambours et des harpes, et dans des guerres considérables il les vaincra.
33 An riga an shirya wurin ƙonawa; an shirya shi saboda sarki. An haƙa ramin wutarsa da zurfi da kuma fāɗi, da isashen wuta da itacen wuta; numfashin Ubangiji, yana kamar kibiritu mai ƙuna, da aka sa masa wuta.
Car Topheth est préparée depuis hier, par le roi préparée, profonde et étendue. Ses aliments sont du feu et beaucoup de bois; le souffle du Seigneur comme un torrent de soufre l’embrase.

< Ishaya 30 >