< Ishaya 30 >

1 “Kaiton’ya’ya masu tayarwa,” in ji Ubangiji, “ga waɗanda suke ƙulle-ƙullen da ba nawa ba, suna yin yarjejjeniya, amma ba ta Ruhuna ba, suna jibga zunubi a kan zunubi;
Malheur, enfants rebelles, dit le Seigneur, vous qui machinez des plans en dehors de moi, contractez des alliances contre mon gré et accumulez ainsi faute sur faute,
2 waɗanda suka gangara zuwa Masar ba tare da sun nemi shawarata; waɗanda suke neman taimakon kāriyar Fir’auna, don neman inuwar mafakar Masar.
vous qui vous mettez en route pour descendre en Egypte, sans avoir demandé mon avis, avec l’espoir de trouver une force dans l’appui de Pharaon et un abri à l’ombre des Egyptiens!
3 Amma kāriyar Fir’auna za tă zama muku abin kunya, inuwar Masar za tă jawo muku kunya.
Mais l’appui de Pharaon sera votre honte, et l’abri à l’ombre des Egyptiens votre déshonneur.
4 Ko da yake suna da shugabanni a Zowan kuma jakadunsu sun iso Hanes,
C’Est que déjà ses princes sont à Çoân, et ses messagers ont atteint Hanès.
5 kowa zai sha kunya saboda mutanen da ba su da amfani gare su, waɗanda ba sa taimako ko amfani, sai dai jawo kunya da da-na-sani.”
Mais tous seront déçus au sujet d’un peuple qui ne leur sera d’aucun secours, qui ne sera ni un appui ni une force, mais seulement une cause de déboire et même d’opprobre.
6 Allah ya faɗa game da dabbobin Negeb cewa, Ta cikin ƙasa mai wahala da mai hatsari inda zakoki da zakanya, inda macizai masu dafi da macizai masu tashi sama suke, jakadu na ɗaukan arzikinsu a kan jakuna, dukiyarsu a kan raƙuma, zuwa ƙasan nan marar riba,
Oracle à propos des animaux du Midi: À travers un pays de détresse et d’angoisse, où vivent lions et lionnes, aspics et dragons volants, ils transportent sur la croupe des ânons leurs richesses, et sur le dos des chameaux leurs trésors, chez un peuple qui n’est d’aucun secours.
7 zuwa Masar, wadda taimakonta marar amfani ne. Saboda haka na yi mata laƙabi Rahab Marar Yin Kome.
L’Appui de l’Egypte, en effet, est vain et illusoire; aussi je dis de cette nation: "Ils font beaucoup de bruit, mais ils restent cois."
8 Tafi yanzu, ka rubuta musu a kan allo, ka rubuta shi a kan littafi, cewa kwanaki suna zuwa zai zama madawwamin shaida.
Maintenant donc rentre, mets cela par écrit sur une tablette en leur présence, fixe-le sur un livre pour durer jusqu’au jour le plus reculé, toujours et toujours.
9 Waɗannan mutane masu tawaye,’ya’ya masu ruɗu,’ya’yan da ba sa niyya su saurara ga umarnan Ubangiji.
Car c’est un peuple indocile, des enfants déloyaux, des enfants qui refusent d’entendre l’enseignement du Seigneur;
10 Sukan ce wa masu gani, “Kada ku ƙara ganin wahayi!” Ga annabawa kuwa sukan ce, “Kada ku ƙara ba mu wahayin abin da yake daidai! Faɗa mana abubuwan da muke so mu ji ne kawai, ku yi annabcin abin da zai ruɗe mu.
Qui disent aux voyants: "Ne voyez point!" et aux prophètes: "Ne nous révélez pas de vérités! Débitez-nous des choses agréables; prophétisez de quoi nourrir nos illusions!
11 Ku bar wannan hanya, ku tashi daga wannan hanya, ku kuma daina kalubalantarmu da Mai Tsarkin nan na Isra’ila!”
Eloignez-vous du chemin, détournez-vous de la route, laissez-nous en paix avec le Saint d’Israël!"
12 Saboda haka, ga abin da Mai Tsarkin nan na Isra’ila yake cewa, “Saboda haka kun ƙi wannan saƙo, kuka dogara ga aikin kama-karya kuka kuma dogara ga yin ruɗu,
C’Est pourquoi le Saint d’Israël parle ainsi: "Puisque vous avez méprisé mes exhortations, placé votre confiance et cherché un appui dans la fraude et le mensonge,
13 wannan zunubi zai zama muku kamar bango mai tsayi, tsagagge da yake kuma fāɗuwa, da zai rushe nan da nan, ba tsammani.
ce crime sera pour vous tel qu’une lézarde menaçante, apparaissant dans un mur élevé qui s’écroule brusquement, en un instant,
14 Zai rushe kucu-kucu kamar tukunyar yumɓu, ya ragargaje ƙaf har cikin gutsattsarinsa ba za a sami ko ɗan katanga don ɗiba garwashin wuta ko a ɗiba ruwa daga tanki ba.”
et qui tombe en ruines comme on brise un vase de potiers, en l’écrasant sans pitié, de telle sorte que dans ses débris on ne peut même ramasser un tesson pour prendre du feu au foyer ou puiser de l’eau à la citerne."
15 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya faɗa, “Cikin tuba da hutu ne kaɗai cetonku yake, cikin shiru da dogara gare ni ne za ku sami ƙarfinku, amma ba za ku sami ko ɗaya a cikinsu ba.
Car ainsi avait parlé le Seigneur, le Dieu éternel, le Saint d’Israël: "C’Est la paix et la douceur qui seront votre salut, la quiétude et la confiance qui seront votre force," mais vous vous y êtes refusés.
16 Kun ce, ‘A’a, za mu gudu a kan dawakai.’ Saboda haka za ku gudu! Kun ce, ‘Za mu hau dawakai masu sauri mu gudu.’ Saboda haka masu fafararku za su fi ku gudu!
Vous disiez: "Non! Nous voulons galoper sur des chevaux," eh bien! Vous galoperez pour fuir "nous voulons monter des coursiers rapides," eh bien! Ils seront rapides, ceux qui courront après vous.
17 Dubu za su gudu don barazanar mutum guda; da jin barazanar mutane biyar dukanku za ku yi ta gudu sai an bar ku kamar sandar tuta a kan dutse, kamar tuta a kan tudu.”
Au nombre de mille, vous fuirez devant la menace d’un seul, devant la menace de cinq, de façon à vous trouver isolés comme un mât sur le sommet de la montagne, comme une bannière sur la hauteur.
18 Duk da haka Ubangiji yana marmari ya yi muku alheri; ya tashi don yă nuna muku jinƙai. Gama Ubangiji Allah ne mai aikata gaskiya. Masu albarka ne dukanku waɗanda suke dogara gare shi!
Pourtant, le Seigneur ne demande qu’à vous rendre sa faveur; pourtant, il se lèvera pour vous prendre en pitié, car le Seigneur est un Dieu de justice: heureux ceux qui espèrent en lui!
19 Ya mutanen Sihiyona, waɗanda suke zama a Urushalima, ba za ku ƙara kuka ba. Zai zama mai alheri sa’ad da kuka yi kukan neman taimako! Da zarar ya ji, zai amsa muku.
Oui, ô peuple de Sion, qui habites dans Jérusalem, tu ne pleureras pas toujours: il accueillera avec bienveillance ta voix suppliante; dès qu’il l’entendra, il te répondra.
20 Ko da yake Ubangiji yakan ba da abincin azaba da ruwan wahala, ba za a ƙara ɓoye malamanku ba; da idanunku za ku gan su.
Le Seigneur vous accordera du pain dans la détresse et de l’eau dans la pénurie; ton guide ne se dérobera plus à ton regard, tes yeux pourront voir ton guide,
21 Ko kun juye dama ko hagu, kunnuwanku za su ji murya a bayanku tana cewa, “Ga hanya; ku yi tafiya a kai.”
et tes oreilles entendre ces paroles qui seront prononcées derrière toi "Voici la route! Suivez-la, que vous preniez à droite ou que vous preniez à gauche."
22 Sa’an nan za ku ƙazantar da gumakanku da kuka dalaye da zinariya; za ku zubar da su kamar rigar al’adar mace ku kuma ce musu, “Ku ɓace mana da gani!”
Alors vous déclarerez impurs le revêtement de vos idoles d’argent et l’enveloppe de vos statues d’or, vous les rejetterez au loin comme des immondices: "Hors d’ici!" leur direz-vous.
23 Zai kuma aiko muku da ruwan sama don shuki a ƙasa, kuma abincin da zai fito daga gona zai zama mai albarka da kuma mai yawa. A wannan rana shanu za su yi kiwo a wadatacciyar makiyaya.
Et Dieu dispensera la pluie à la semence que vous confierez au sol le pain que produira la terre sera substantiel et savoureux, tes troupeaux paîtront en ce jour dans de vastes prairies.
24 Shanunku da jakunanku da suke huɗar gonakinku za su ci harawa mafi kyau, wanda an sheƙe shi da babban cokali mai yatsu da kuma babban cokali.
Les bœufs et les ânes, employés aux travaux des champs, mangeront un fourrage assaisonné de sel et qu’on aura vanné avec la pelle et le van.
25 A ranar babban kisa, sa’ad da hasumiyoyi za su fāɗi, rafuffukan ruwa za su malalo a kan kowane dutse da kowane tudu mai tsawo.
Sur toute haute montagne et sur toute colline élevée, il y aura des ruisseaux, des eaux courantes, au jour du grand massacre, lors de la chute des tours fortifiées.
26 Wata zai yi haske kamar rana, kuma hasken rana zai ma yi sau bakwai na haskenta, kamar hasken cikakku ranaku bakwai, sa’ad da Ubangiji zai ɗaura raunukan mutanensa ya kuma warkar da raunukan da ya yi musu.
La lune, alors, brillera du même éclat que le soleil, et la lumière du soleil sera sept fois plus vive, comme la lumière des sept jours, à l’époque où l’Eternel pansera les blessures de son peuple et guérira les meurtrissures qui l’ont atteint.
27 Duba, Sunan Ubangiji yana zuwa daga nesa, tare da fushi mai ƙuna da kuma baƙin hayaƙi; leɓunansa sun cika da fushi, harshensa kuma wuta ce mai cinyewa.
Voici la majesté de l’Eternel qui s’avance de loin: ardente est sa colère, pesant le tourbillon de fumée qui s’élève, ses lèvres sont chargées de courroux, sa langue est comme un feu dévorant,
28 Numfashinsa kamar raƙuman ruwa masu gudu yana tashi har zuwa wuya. Yakan tankaɗe al’ummai cikin lariyar hallaka; yakan sa a muƙamuƙan mutane linzamin da zai jagorance su su kauce.
son souffle comme un torrent impétueux qui monte jusqu’au cou: il va secouer les peuples dans le van de la destruction et poser entre les mâchoires des peuples un frein qui les dirige de travers.
29 Za ku kuma rera kamar a daren da kuke shagalin biki mai tsarki; zukatanku za su yi farin ciki kamar sa’ad da mutane sukan haura da busa zuwa dutsen Ubangiji, zuwa Dutse na Isra’ila.
Parmi vous retentiront des chants, comme dans la nuit consacrée à une fête; vous aurez le cœur joyeux comme les pèlerins qui, au son de la flûte, se rendent sur la montagne de l’Eternel auprès du rocher d’Israël.
30 Ubangiji zai sa mutane su ji muryarsa mai daraja ya kuma sa su ga hannunsa na saukowa tare da fushi mai ƙuna da kuma wuta mai cinyewa, gizagizai za su ɓarke, za a yi hadarin tsawa da ƙanƙara.
Dieu fera éclater sa voix majestueuse et sentir la pesanteur de son bras qui s’abat, dans un déchaînement de colère, dans l’embrasement d’un feu dévorant, accompagné de tempêtes, de pluies violentes et de grêlons.
31 Muryar Ubangiji za tă firgita Assuriya da sandar mulkinsa zai kashe su.
Aussi à la voix de l’Eternel, Achour sera pris de terreur, tandis que Dieu le frappera de son bâton.
32 Kowane bugun da Ubangiji zai yi musu da bulalarsa na hukunci zai zama kiɗi ga ganguna da garaya, yayinda yake yaƙi da su da naushin hannunsa.
Et chaque fois que retombera ce bâton prédestiné, que l’Eternel brandit contre lui, on entendra des tambourins et des harpes. Ce sont des combats acharnés que lui livrera Dieu.
33 An riga an shirya wurin ƙonawa; an shirya shi saboda sarki. An haƙa ramin wutarsa da zurfi da kuma fāɗi, da isashen wuta da itacen wuta; numfashin Ubangiji, yana kamar kibiritu mai ƙuna, da aka sa masa wuta.
Car dès longtemps le Tofet est tout prêt; il a été disposé, lui aussi, profond et large, pour le roi, avec son bûcher allumé, où le bois abonde et que fait flamber le souffle de l’Eternel, tel qu’un torrent de soufre.

< Ishaya 30 >