< Ishaya 30 >

1 “Kaiton’ya’ya masu tayarwa,” in ji Ubangiji, “ga waɗanda suke ƙulle-ƙullen da ba nawa ba, suna yin yarjejjeniya, amma ba ta Ruhuna ba, suna jibga zunubi a kan zunubi;
Malheur aux enfants rebelles, — oracle de Yahweh, qui font des projets, mais sans moi; qui contractent des pactes, mais sans mon esprit, accumulant péché sur péché.
2 waɗanda suka gangara zuwa Masar ba tare da sun nemi shawarata; waɗanda suke neman taimakon kāriyar Fir’auna, don neman inuwar mafakar Masar.
Ils descendent sur le chemin de l’Égypte, sans avoir consulté ma bouche, pour se réfugier sous la protection de Pharaon et pour s’abriter à l’ombre de l’Égypte!
3 Amma kāriyar Fir’auna za tă zama muku abin kunya, inuwar Masar za tă jawo muku kunya.
La protection de Pharaon sera pour vous une honte; et le refuge à l’ombre de l’Égypte, une confusion.
4 Ko da yake suna da shugabanni a Zowan kuma jakadunsu sun iso Hanes,
Déjà les princes de Juda sont à Tanis, et ses envoyés se sont avancés jusqu’à Hanés;
5 kowa zai sha kunya saboda mutanen da ba su da amfani gare su, waɗanda ba sa taimako ko amfani, sai dai jawo kunya da da-na-sani.”
tous sont confus à cause d’un peuple qui ne leur sert de rien, qui ne leur donne ni aide ni secours, mais seulement confusion et ignominie. —
6 Allah ya faɗa game da dabbobin Negeb cewa, Ta cikin ƙasa mai wahala da mai hatsari inda zakoki da zakanya, inda macizai masu dafi da macizai masu tashi sama suke, jakadu na ɗaukan arzikinsu a kan jakuna, dukiyarsu a kan raƙuma, zuwa ƙasan nan marar riba,
Oracle des bêtes du négéb: A travers une contrée de détresse et d’angoisse, d’où sortent le lion et la lionne, la vipère et le dragon volant, ils portent leurs richesses sur le dos des ânes, et leurs trésors sur la bosse des chameaux, à un peuple qui ne sert à rien.
7 zuwa Masar, wadda taimakonta marar amfani ne. Saboda haka na yi mata laƙabi Rahab Marar Yin Kome.
Le secours de l’Égypte sera vanité et néant, c’est pourquoi je la nomme: « La superbe qui reste assise. »
8 Tafi yanzu, ka rubuta musu a kan allo, ka rubuta shi a kan littafi, cewa kwanaki suna zuwa zai zama madawwamin shaida.
Va maintenant, grave cela sur une tablette en leur présence, et écris-le dans un livre, afin que ce soit, pour les jours à venir, un témoignage à perpétuité.
9 Waɗannan mutane masu tawaye,’ya’ya masu ruɗu,’ya’yan da ba sa niyya su saurara ga umarnan Ubangiji.
Car c’est un peuple de rébellion, ce sont des enfants infidèles, des enfants qui refusent d’écouter la loi de Yahweh.
10 Sukan ce wa masu gani, “Kada ku ƙara ganin wahayi!” Ga annabawa kuwa sukan ce, “Kada ku ƙara ba mu wahayin abin da yake daidai! Faɗa mana abubuwan da muke so mu ji ne kawai, ku yi annabcin abin da zai ruɗe mu.
Ils disent aux voyants: « Ne voyez point; » et aux prophètes: « Ne nous prophétisez pas la vérité; dites-nous des choses agréables, prophétisez des illusions!
11 Ku bar wannan hanya, ku tashi daga wannan hanya, ku kuma daina kalubalantarmu da Mai Tsarkin nan na Isra’ila!”
Ecartez-vous de la voie, détournez-vous du chemin; ôtez de devant nos yeux le Saint d’Israël! » —
12 Saboda haka, ga abin da Mai Tsarkin nan na Isra’ila yake cewa, “Saboda haka kun ƙi wannan saƙo, kuka dogara ga aikin kama-karya kuka kuma dogara ga yin ruɗu,
C’est pourquoi ainsi parle le Saint d’Israël: Puisque vous méprisez cette parole et que vous vous confiez dans la violence et l’artifice, et que vous en faites votre appui,
13 wannan zunubi zai zama muku kamar bango mai tsayi, tsagagge da yake kuma fāɗuwa, da zai rushe nan da nan, ba tsammani.
à cause de cela, cette iniquité sera pour vous comme une lézarde qui menace ruine et fait saillie sur un mur élevé, dont soudain, en un instant, l’écroulement se produit.
14 Zai rushe kucu-kucu kamar tukunyar yumɓu, ya ragargaje ƙaf har cikin gutsattsarinsa ba za a sami ko ɗan katanga don ɗiba garwashin wuta ko a ɗiba ruwa daga tanki ba.”
Il se brise comme se brise un vase d’argile, que l’on fracasse sans pitié, sans que l’on trouve dans ses débris un morceau, pour prendre du feu au brasier, ou puiser de l’eau à la citerne.
15 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya faɗa, “Cikin tuba da hutu ne kaɗai cetonku yake, cikin shiru da dogara gare ni ne za ku sami ƙarfinku, amma ba za ku sami ko ɗaya a cikinsu ba.
Car ainsi a parlé le Seigneur Yahweh, le Saint d’Israël: Par la conversion et une paisible attente vous seriez sauvés; dans le repos et la confiance serait votre force. Mais vous ne l’avez pas voulu
16 Kun ce, ‘A’a, za mu gudu a kan dawakai.’ Saboda haka za ku gudu! Kun ce, ‘Za mu hau dawakai masu sauri mu gudu.’ Saboda haka masu fafararku za su fi ku gudu!
et vous avez dit: « Non! Mais nous fuirons sur des chevaux! » — eh bien, vous fuirez — « Nous volerons sur des coursiers! » — eh bien, ceux qui vous poursuivront seront plus rapides!
17 Dubu za su gudu don barazanar mutum guda; da jin barazanar mutane biyar dukanku za ku yi ta gudu sai an bar ku kamar sandar tuta a kan dutse, kamar tuta a kan tudu.”
Mille à la menace d’un seul, et à la menace de cinq, vous fuirez, jusqu’à ce que vous ne soyez plus qu’un reste, semblable à un mât sur le sommet de la montagne, à un signal sur la colline.
18 Duk da haka Ubangiji yana marmari ya yi muku alheri; ya tashi don yă nuna muku jinƙai. Gama Ubangiji Allah ne mai aikata gaskiya. Masu albarka ne dukanku waɗanda suke dogara gare shi!
C’est pourquoi Yahweh attend pour vous faire grâce, c’est pourquoi il se lèvera pour vous faire miséricorde; car Yahweh est un Dieu juste. Heureux tous ceux qui espèrent en lui!
19 Ya mutanen Sihiyona, waɗanda suke zama a Urushalima, ba za ku ƙara kuka ba. Zai zama mai alheri sa’ad da kuka yi kukan neman taimako! Da zarar ya ji, zai amsa muku.
Car, ô peuple qui habite en Sion, à Jérusalem, tu ne pleureras désormais plus. A ton premier cri, il te fera grâce; dès qu’il t’aura entendu, il t’exaucera.
20 Ko da yake Ubangiji yakan ba da abincin azaba da ruwan wahala, ba za a ƙara ɓoye malamanku ba; da idanunku za ku gan su.
Le Seigneur vous donnera le pain de l’angoisse et l’eau de la détresse; et ceux qui t’instruisent ne se cacheront plus et tes yeux verront ceux qui t’instruisent;
21 Ko kun juye dama ko hagu, kunnuwanku za su ji murya a bayanku tana cewa, “Ga hanya; ku yi tafiya a kai.”
et tes oreilles entendront derrière toi la voix qui dira: « Voici le chemin, suivez-le! » quand vous vous détournerez à droite ou à gauche.
22 Sa’an nan za ku ƙazantar da gumakanku da kuka dalaye da zinariya; za ku zubar da su kamar rigar al’adar mace ku kuma ce musu, “Ku ɓace mana da gani!”
Vous traiterez comme impurs l’argent qui recouvre vos idoles, et l’or qui revêt vos statues; vous les rejetterez comme une chose souillée: « Hors d’ici! » leur direz-vous.
23 Zai kuma aiko muku da ruwan sama don shuki a ƙasa, kuma abincin da zai fito daga gona zai zama mai albarka da kuma mai yawa. A wannan rana shanu za su yi kiwo a wadatacciyar makiyaya.
Le Seigneur enverra ses ondées sur la semence que tu auras semée en terre, et le pain que donnera la terre sera délicieux et abondant; tes troupeaux en ce jour-là paîtront dans de vastes pâturages;
24 Shanunku da jakunanku da suke huɗar gonakinku za su ci harawa mafi kyau, wanda an sheƙe shi da babban cokali mai yatsu da kuma babban cokali.
et les bœufs et les ânes, qui travaillent la terre, mangeront un fourrage savoureux vanné avec la pelle et le van.
25 A ranar babban kisa, sa’ad da hasumiyoyi za su fāɗi, rafuffukan ruwa za su malalo a kan kowane dutse da kowane tudu mai tsawo.
Et sur toute haute montagne, et sur toute colline élevée, il y aura des ruisseaux, des courants d’eau, au jour du grand carnage quand les tours tomberont.
26 Wata zai yi haske kamar rana, kuma hasken rana zai ma yi sau bakwai na haskenta, kamar hasken cikakku ranaku bakwai, sa’ad da Ubangiji zai ɗaura raunukan mutanensa ya kuma warkar da raunukan da ya yi musu.
La lumière de la lune sera comme la lumière du soleil, et la lumière du soleil sera sept fois plus grande, comme la lumière de sept jours, au jour où Yahweh bandera la blessure de son peuple, et guérira les plaies dont il l’avait frappé.
27 Duba, Sunan Ubangiji yana zuwa daga nesa, tare da fushi mai ƙuna da kuma baƙin hayaƙi; leɓunansa sun cika da fushi, harshensa kuma wuta ce mai cinyewa.
Voici que le nom de Yahweh vient de loin, sa colère brûle, et l’ardeur en est accablante; ses lèvres respirent la fureur, et sa langue est comme un feu dévorant.
28 Numfashinsa kamar raƙuman ruwa masu gudu yana tashi har zuwa wuya. Yakan tankaɗe al’ummai cikin lariyar hallaka; yakan sa a muƙamuƙan mutane linzamin da zai jagorance su su kauce.
Son souffle est comme un torrent débordé, qui monte jusqu’au cou, pour cribler les nations avec le crible de la destruction, et mettre un frein d’égarement aux mâchoires des peuples.
29 Za ku kuma rera kamar a daren da kuke shagalin biki mai tsarki; zukatanku za su yi farin ciki kamar sa’ad da mutane sukan haura da busa zuwa dutsen Ubangiji, zuwa Dutse na Isra’ila.
Alors vous entonnerez des cantiques comme dans la nuit où l’on célèbre la fête, et vous aurez le cœur joyeux, comme celui qui monte au son de la flûte, pour aller à la montagne de Yahweh, vers le rocher d’Israël.
30 Ubangiji zai sa mutane su ji muryarsa mai daraja ya kuma sa su ga hannunsa na saukowa tare da fushi mai ƙuna da kuma wuta mai cinyewa, gizagizai za su ɓarke, za a yi hadarin tsawa da ƙanƙara.
Yahweh fera éclater la majesté de sa voix, et il fera voir son bras qui s’abaisse, dans l’ardeur de sa colère, et la flamme d’un feu dévorant, dans la tempête, l’averse et les pierres de grêle.
31 Muryar Ubangiji za tă firgita Assuriya da sandar mulkinsa zai kashe su.
Et Assur tremblera à la voix de Yahweh; il frappera de sa verge,
32 Kowane bugun da Ubangiji zai yi musu da bulalarsa na hukunci zai zama kiɗi ga ganguna da garaya, yayinda yake yaƙi da su da naushin hannunsa.
et, à chaque fois que passera la verge fatale, que Yahweh abaissera sur lui, on fera retentir les tambourins et les harpes, et il combattra contre lui à coups redoublés.
33 An riga an shirya wurin ƙonawa; an shirya shi saboda sarki. An haƙa ramin wutarsa da zurfi da kuma fāɗi, da isashen wuta da itacen wuta; numfashin Ubangiji, yana kamar kibiritu mai ƙuna, da aka sa masa wuta.
Car Topheth est dès longtemps préparé; lui aussi est prêt pour le roi; le Seigneur l’a fait large et profond; il y a sur son bûcher du feu et du bois en abondance; le souffle de Yahweh, comme un torrent de soufre, l’embrase.

< Ishaya 30 >