< Ishaya 30 >
1 “Kaiton’ya’ya masu tayarwa,” in ji Ubangiji, “ga waɗanda suke ƙulle-ƙullen da ba nawa ba, suna yin yarjejjeniya, amma ba ta Ruhuna ba, suna jibga zunubi a kan zunubi;
Tragedy is coming to my defiant children, declares the Lord. You make plans that don't come from me; you make alliances against my wishes, adding sin to sin.
2 waɗanda suka gangara zuwa Masar ba tare da sun nemi shawarata; waɗanda suke neman taimakon kāriyar Fir’auna, don neman inuwar mafakar Masar.
You go to Egypt without asking me, looking to Pharaoh for protection, hoping to find safety hiding behind Egypt.
3 Amma kāriyar Fir’auna za tă zama muku abin kunya, inuwar Masar za tă jawo muku kunya.
But the protection of Pharaoh will be an embarrassment to you; hiding behind Egypt will only bring you humiliation.
4 Ko da yake suna da shugabanni a Zowan kuma jakadunsu sun iso Hanes,
Even though he has officials at Zoan and his messengers reach Hanes,
5 kowa zai sha kunya saboda mutanen da ba su da amfani gare su, waɗanda ba sa taimako ko amfani, sai dai jawo kunya da da-na-sani.”
the Egyptians will offend everyone because they are useless—they're no help and good for nothing, except for causing shame and bringing disgrace.
6 Allah ya faɗa game da dabbobin Negeb cewa, Ta cikin ƙasa mai wahala da mai hatsari inda zakoki da zakanya, inda macizai masu dafi da macizai masu tashi sama suke, jakadu na ɗaukan arzikinsu a kan jakuna, dukiyarsu a kan raƙuma, zuwa ƙasan nan marar riba,
A message about the animals of the Negev. The messengers travel through a harsh and hostile land where lions and lionesses live, vipers and vicious snakes too. Their donkeys are burdened down with valuable gifts, their camels are loaded with treasure, to give to a worthless people that can't help.
7 zuwa Masar, wadda taimakonta marar amfani ne. Saboda haka na yi mata laƙabi Rahab Marar Yin Kome.
Egypt's support is an empty breath of wind. That's why I call her Pride Sitting Down.
8 Tafi yanzu, ka rubuta musu a kan allo, ka rubuta shi a kan littafi, cewa kwanaki suna zuwa zai zama madawwamin shaida.
Now go and write all this down on a tablet and on a scroll so that it will last forever and ever.
9 Waɗannan mutane masu tawaye,’ya’ya masu ruɗu,’ya’yan da ba sa niyya su saurara ga umarnan Ubangiji.
For they are a rebellious people, deceitful children, who refuse to listen to the Lord's instructions.
10 Sukan ce wa masu gani, “Kada ku ƙara ganin wahayi!” Ga annabawa kuwa sukan ce, “Kada ku ƙara ba mu wahayin abin da yake daidai! Faɗa mana abubuwan da muke so mu ji ne kawai, ku yi annabcin abin da zai ruɗe mu.
They tell people who see visions, “Stop seeing visions!” and to the prophets, “Don't give us prophecies about doing right—just tell us pleasant things and give us fake prophecies.
11 Ku bar wannan hanya, ku tashi daga wannan hanya, ku kuma daina kalubalantarmu da Mai Tsarkin nan na Isra’ila!”
Stop telling us straight; go a different direction! We don't want to hear any more about the Holy One of Israel.”
12 Saboda haka, ga abin da Mai Tsarkin nan na Isra’ila yake cewa, “Saboda haka kun ƙi wannan saƙo, kuka dogara ga aikin kama-karya kuka kuma dogara ga yin ruɗu,
So this is how the Holy One of Israel replies, Since you have rejected this message, and since you trust in oppression and believe in dishonesty,
13 wannan zunubi zai zama muku kamar bango mai tsayi, tsagagge da yake kuma fāɗuwa, da zai rushe nan da nan, ba tsammani.
your punishment will suddenly fall on you, like a high wall that bulges out and collapses in an instant.
14 Zai rushe kucu-kucu kamar tukunyar yumɓu, ya ragargaje ƙaf har cikin gutsattsarinsa ba za a sami ko ɗan katanga don ɗiba garwashin wuta ko a ɗiba ruwa daga tanki ba.”
You will be smashed like a clay pot, broken into such tiny pieces that there won't be a big enough piece to pick up coals from a hearth or a little bit of water from a well.
15 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya faɗa, “Cikin tuba da hutu ne kaɗai cetonku yake, cikin shiru da dogara gare ni ne za ku sami ƙarfinku, amma ba za ku sami ko ɗaya a cikinsu ba.
This is what the Lord God, the Holy One of Israel, said, If you repent and patiently trust in me, you would be saved; you would be strong if you had such calm confidence. But you refused to do it.
16 Kun ce, ‘A’a, za mu gudu a kan dawakai.’ Saboda haka za ku gudu! Kun ce, ‘Za mu hau dawakai masu sauri mu gudu.’ Saboda haka masu fafararku za su fi ku gudu!
You replied, “No! We'll escape on horseback! We'll get away on fast horses!” But the fast ones will be the ones chasing you!
17 Dubu za su gudu don barazanar mutum guda; da jin barazanar mutane biyar dukanku za ku yi ta gudu sai an bar ku kamar sandar tuta a kan dutse, kamar tuta a kan tudu.”
Just one of them will chase after a thousand of you. Just five of them will make you all run away. All that will be left of you will look like a flag fluttering on the top of a mountain, a banner waving on a hill.
18 Duk da haka Ubangiji yana marmari ya yi muku alheri; ya tashi don yă nuna muku jinƙai. Gama Ubangiji Allah ne mai aikata gaskiya. Masu albarka ne dukanku waɗanda suke dogara gare shi!
So the Lord waits, wanting to be kind to you, ready to act to show you mercy, for the Lord is a God who does what is right. All who wait for him are blessed.
19 Ya mutanen Sihiyona, waɗanda suke zama a Urushalima, ba za ku ƙara kuka ba. Zai zama mai alheri sa’ad da kuka yi kukan neman taimako! Da zarar ya ji, zai amsa muku.
People of Zion, you who live in Jerusalem, you won't have to weep any more. When you cry for help he will be kind to you. He will answer you immediately he hears you.
20 Ko da yake Ubangiji yakan ba da abincin azaba da ruwan wahala, ba za a ƙara ɓoye malamanku ba; da idanunku za ku gan su.
Even though the Lord will give you the bread of hardship to eat and the water of suffering to drink, your teacher will no longer hide himself from you—you will see him with your own eyes.
21 Ko kun juye dama ko hagu, kunnuwanku za su ji murya a bayanku tana cewa, “Ga hanya; ku yi tafiya a kai.”
When you walk to the right or to the left, you will hear this command coming from behind you: “This is the way to follow.”
22 Sa’an nan za ku ƙazantar da gumakanku da kuka dalaye da zinariya; za ku zubar da su kamar rigar al’adar mace ku kuma ce musu, “Ku ɓace mana da gani!”
You will defile your silver-coated idols coated with silver and your gold-covered images. You will throw them away like a dirty cloth used for periods, and say to them, “out of here!”
23 Zai kuma aiko muku da ruwan sama don shuki a ƙasa, kuma abincin da zai fito daga gona zai zama mai albarka da kuma mai yawa. A wannan rana shanu za su yi kiwo a wadatacciyar makiyaya.
He will send rain when you sow, and the land will produce great harvests. At that time your cattle will feed in rich pastures.
24 Shanunku da jakunanku da suke huɗar gonakinku za su ci harawa mafi kyau, wanda an sheƙe shi da babban cokali mai yatsu da kuma babban cokali.
The oxen and donkeys that help cultivate the earth will eat good greens and grain, spread with fork and shovel.
25 A ranar babban kisa, sa’ad da hasumiyoyi za su fāɗi, rafuffukan ruwa za su malalo a kan kowane dutse da kowane tudu mai tsawo.
At that time when your enemies are killed and the fortresses fall, streams of water will flow down every mountain and hill.
26 Wata zai yi haske kamar rana, kuma hasken rana zai ma yi sau bakwai na haskenta, kamar hasken cikakku ranaku bakwai, sa’ad da Ubangiji zai ɗaura raunukan mutanensa ya kuma warkar da raunukan da ya yi musu.
The moon will shine as bright as the sun, and the sun will shine seven times brighter, like having seven days light in one. This is the way it will be when the Lord bandages the injuries of his people and heals the wounds he caused them.
27 Duba, Sunan Ubangiji yana zuwa daga nesa, tare da fushi mai ƙuna da kuma baƙin hayaƙi; leɓunansa sun cika da fushi, harshensa kuma wuta ce mai cinyewa.
Look how the Lord arrives from far away, burning with anger and accompanied by thick clouds of smoke! What he says shows his anger—it's like a fire that burns everything up.
28 Numfashinsa kamar raƙuman ruwa masu gudu yana tashi har zuwa wuya. Yakan tankaɗe al’ummai cikin lariyar hallaka; yakan sa a muƙamuƙan mutane linzamin da zai jagorance su su kauce.
His breath rushes out like a flood that comes up to the neck. He shakes the nations in a sieve that destroys them; he puts bridles in the mouths of the different peoples to lead them away.
29 Za ku kuma rera kamar a daren da kuke shagalin biki mai tsarki; zukatanku za su yi farin ciki kamar sa’ad da mutane sukan haura da busa zuwa dutsen Ubangiji, zuwa Dutse na Isra’ila.
But you will have a song to sing like you do on the night of a holy festival. You will celebrate in happiness like those who play pipes as they go up to the mountain of the Lord, to the Rock of Israel.
30 Ubangiji zai sa mutane su ji muryarsa mai daraja ya kuma sa su ga hannunsa na saukowa tare da fushi mai ƙuna da kuma wuta mai cinyewa, gizagizai za su ɓarke, za a yi hadarin tsawa da ƙanƙara.
The Lord will shout so everyone hears him he will reveal his great power. He will hit out in his anger and fury, with a fire that burns everything up, and with torrential rain, storm, and hail.
31 Muryar Ubangiji za tă firgita Assuriya da sandar mulkinsa zai kashe su.
At the Lord's command the Assyrians will be shattered, knocked down by his scepter.
32 Kowane bugun da Ubangiji zai yi musu da bulalarsa na hukunci zai zama kiɗi ga ganguna da garaya, yayinda yake yaƙi da su da naushin hannunsa.
Every time the Lord hits them with his rod of punishment it will be accompanied by the music of tambourines and harps as he fights them, swinging into them in battle.
33 An riga an shirya wurin ƙonawa; an shirya shi saboda sarki. An haƙa ramin wutarsa da zurfi da kuma fāɗi, da isashen wuta da itacen wuta; numfashin Ubangiji, yana kamar kibiritu mai ƙuna, da aka sa masa wuta.
The place of burning has been prepared a long time ago, ready for the king. Its funeral pyre is deep and wide, and has plenty of fire and wood. The breath of the Lord, like a flood of burning sulfur, sets it on fire.