< Ishaya 3 >

1 Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,
Jer gle, Gospod, Gospod nad vojskama uzeæe Jerusalimu i Judi potporu i pomoæ, svaku potporu u hljebu i svaku potporu u vodi,
2 jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,
Junaka i vojnika, sudiju i proroka, i mudarca i starca,
3 shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.
Pedesetnika i ugledna èovjeka, i savjetnika i vješta umjetnika i èovjeka rjeèita.
4 “Zan sa’yan yara su zama shugabanninsu;’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”
I daæu im knezove mladiæe, i djeca æe im biti gospodari.
5 Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.
I èiniæe silu u narodu jedan drugome i svaki bližnjemu svojemu; dijete æe ustajati na starca i nepošten èovjek na poštena.
6 Mutum zai kama ɗaya daga cikin’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”
I èovjek æe uhvatiti brata svojega iz kuæe oca svojega govoreæi: imaš haljinu, budi nam knez, ovaj rasap neka je pod tvojom rukom.
7 Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”
A on æe se zakleti u onaj dan govoreæi: neæu biti ljekar, niti imam kod kuæe hljeba ni haljine, ne postavljajte me knezom narodu.
8 Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.
Jer se obori Jerusalim i Juda pade, jer se jezik njihov i djela njihova protive Gospodu da draže oèi slave njegove.
9 Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.
Što se vidi na licu njihovu svjedoèi na njih, razglašuju grijeh svoj kao Sodom, ne taje; teško duši njihovoj! jer sami sebi èine zlo.
10 Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.
Recite pravedniku da æe mu dobro biti, jer æe jesti plod od djela svojih.
11 Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.
Teško bezbožniku! zlo æe mu biti, jer æe mu se naplatiti ruke njegove.
12 Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.
Narodu mojemu èine silu djeca, i žene su im gospodari. Narode moj! koji te vode, zavode te, i kvare put hoda tvojega.
13 Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.
Ustaje Gospod na parbu, stoji da sudi narodima.
14 Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.
Gospod æe doæi na sud sa starješinama naroda svojega i s knezovima njegovijem, jer vi potrste vinograd, grabež od siromaha u vašim je kuæama.
15 Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
Zašto gazite narod moj i lice siromasima satirete? govori Gospod, Gospod nad vojskama.
16 Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
Još govori Gospod: što se poniješe kæeri Sionske i idu opružena vrata i namigujuæi oèima, sitno koraèaju i zvekeæu nogama,
17 Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
Zato æe Gospod uèiniti da oæelavi tjeme kæerima Sionskim, i otkriæe Gospod golotinju njihovu.
18 A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
Tada æe Gospod skinuti nakit s obuæe i vezove i mjeseèiæe,
19 ’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
Nizove i lanèiæe i trepetljike,
20 kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
Ukosnike i podveze i pojase i stakalca mirisna i oboce,
21 da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
Prstene i poèeonike,
22 tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
Sveèane haljine i ogrtaèe i prijevjese i toboce,
23 da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
I ogledala i košuljice i oglavlja i pokrivala.
24 A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
I mjesto mirisa biæe smrad, i mjesto pojasa raspojasina, mjesto pletenica æela, mjesto širokih skuta pripasana vreæa, i mjesto ljepote ogorjelina.
25 Mazanku za su mutu ta wurin takobi, jarumawanku za su mutu a yaƙi.
Tvoji æe ljudi pasti od maèa i junaci tvoji u ratu.
26 Ƙofofin Sihiyona za su yi makoki su kuma yi kuka; za tă zama wofi, za tă zauna a ƙasa.
I tužiæe i plakaæe vrata njegova, a on æe pust ležati na zemlji.

< Ishaya 3 >