< Ishaya 3 >

1 Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,
خداوند، خدای لشکرهای آسمان، به‌زودی رزق و روزی اورشلیم و یهودا را قطع خواهد کرد و بزرگان مملکت را از میان برخواهد داشت. قحطی نان و آب خواهد بود.
2 jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,
جنگاوران و سپاهیان، داوران و انبیا، فالگیران و ریش‌سفیدان،
3 shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.
سرداران و اشراف‌زادگان و حکیمان، صنعتگران ماهر و جادوگران زبردست، همگی از بین خواهند رفت.
4 “Zan sa’yan yara su zama shugabanninsu;’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”
به جای آنان، کودکان مملکت را اداره خواهند کرد.
5 Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.
همه جا هرج و مرج خواهد بود و هر کس حق دیگری را پایمال خواهد نمود. همسایه با همسایه به نزاع خواهد پرداخت، جوانان احترام پیران را نگه نخواهند داشت و اشخاص پست علیه انسانهای شریف برخواهند خاست.
6 Mutum zai kama ɗaya daga cikin’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”
روزی خواهد رسید که افراد یک خاندان، یکی را از بین خود انتخاب کرده، خواهند گفت: «تو لباس اضافه داری، پس در این ویرانی رهبر ما باش.»
7 Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”
او جواب خواهد داد: «نه، هیچ کمکی از دست من برنمی‌آید! من نیز خوراک و پوشاک ندارم. مرا رهبر خود نکنید!»
8 Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.
آری، اورشلیم خراب خواهد شد و یهودا از بین خواهد رفت، زیرا مردم بر ضد خداوند سخن می‌گویند و عمل می‌کنند و به حضور پرجلال او اهانت می‌نمایند.
9 Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.
چهرهٔ آنان راز درونشان را فاش می‌سازد و نشان می‌دهد که گناهکارند. آنان مانند مردم سدوم و عموره آشکارا گناه می‌کنند. وای بر آنان، زیرا با این کارهای زشت، خود را دچار مصیبت کرده‌اند.
10 Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.
به عادلان بگویید: «سعادتمندی نصیب شما خواهد شد و از ثمرهٔ کارهای خود بهره‌مند خواهید گردید.»
11 Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.
ولی به شریران بگویید: «وای بر شما، زیرا مصیبت نصیب شما خواهد شد و به سزای اعمالتان خواهید رسید.»
12 Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.
ای قوم من، رهبران شما کودکانند و حاکمانتان زنان. آنان شما را به گمراهی و نابودی می‌کشانند.
13 Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.
خداوند برخاسته تا قوم خود را محاکمه و داوری کند.
14 Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.
او بزرگان و رهبران قوم را محاکمه خواهد کرد، زیرا آنان تاکستانهای فقیران را غارت کرده، انبارهای خود را پر ساخته‌اند.
15 Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
خداوند لشکرهای آسمان می‌فرماید: «شما را چه شده است که اینچنین بر قوم من ستم می‌کنید و آنان را به خاک و خون می‌کشید؟»
16 Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
خداوند زنان مغرور صهیون را نیز محاکمه خواهد کرد. آنان با عشوه راه می‌روند و النگوهای خود را به صدا در می‌آورند و با چشمان شهوت‌انگیز در میان جماعت پرسه می‌زنند.
17 Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
خداوند بلای گری بر این زنان خواهد فرستاد تا سرهایشان کچل و بی‌مو شوند.
18 A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
در آن روز خداوند تمام زینت‌آلاتشان را از ایشان خواهد گرفت گوشواره‌ها، النگوها، روبندها،
19 ’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
20 kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
کلاهها، زینت پاها، دعاهایی که بر کمر و بازو می‌بندند، عطردانها،
21 da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
انگشترها و حلقه‌های زینتی بینی،
22 tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
لباسهای نفیس و بلند، شالها، کیفها،
23 da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
آئینه‌ها، دستمالهای زیبای کتان، روسریها و چادرها. آری، خداوند از همهٔ اینها محرومشان خواهد کرد.
24 A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
به جای بوی خوش عطر، بوی گند تعفن خواهند داد. به جای کمربند، طناب به کمر خواهند بست. به جای لباسهای بلند و زیبا، لباس عزا خواهند پوشید. تمام موهای زیبایشان خواهد ریخت و زیبایی‌شان به رسوایی تبدیل خواهد شد.
25 Mazanku za su mutu ta wurin takobi, jarumawanku za su mutu a yaƙi.
شوهرانشان در میدان جنگ کشته خواهند شد
26 Ƙofofin Sihiyona za su yi makoki su kuma yi kuka; za tă zama wofi, za tă zauna a ƙasa.
و شهر متروک شده، در سوگ آنان خواهد نشست و ناله سر خواهد داد.

< Ishaya 3 >