< Ishaya 3 >
1 Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,
For se, Herren, Israels Gud, hærskarenes Gud, tar bort fra Jerusalem og Juda støtte og stav, hver støtte av brød og hver støtte av vann,
2 jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,
helt og krigsmann, dommer og profet, spåmann og eldste,
3 shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.
høvedsmann over femti og hver høit aktet mann, rådsherre og håndverksmester og kyndig åndemaner.
4 “Zan sa’yan yara su zama shugabanninsu;’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”
Og jeg vil sette barn til styrere over dem, og guttekåthet skal herske over dem.
5 Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.
Blandt folket skal den ene undertrykke den andre, hver mann sin næste; den unge skal sette sig op mot den gamle, den ringeaktede mot den høit ærede.
6 Mutum zai kama ɗaya daga cikin’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”
Når en da tar fatt på en annen i hans fars hus og sier: Du har en kappe, du skal være vår fyrste, og denne ruin skal være under din hånd,
7 Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”
så skal han samme dag svare og si: Jeg vil ikke være læge, og i mitt hus er det intet brød og ingen klær; I skal ikke sette mig til folkets fyrste.
8 Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.
For Jerusalem snubler, og Juda faller, fordi deres tunge og deres gjerninger er mot Herren, de trosser hans herlighets øine.
9 Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.
Uttrykket i deres ansikter vidner mot dem, og om sin synd taler de åpent som folket i Sodoma, de dølger den ikke; ve deres sjeler, for de volder sig selv ulykke!
10 Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.
Si om den rettferdige at det går ham godt! For han skal ete frukten av sine gjerninger.
11 Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.
Ve den ugudelige! Ham går det ille; for det hans hender har gjort, skal gjøres mot ham selv.
12 Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.
Mitt folks herskere er barn, og kvinner råder over det. Mitt folk! Dine førere er forførere, og den vei du skal gå, har de ødelagt.
13 Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.
Herren treder frem for å føre sak, og han står der for å dømme folkene.
14 Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.
Herren møter i retten sitt folks eldste og dets høvdinger: I har avgnaget vingården! I har rov fra de fattige i husene hos eder!
15 Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
Hvorledes kan I tråkke mitt folk ned og knuse de fattige? sier Herren, Israels Gud, hærskarenes Gud.
16 Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
Og Herren sa: Fordi Sions døtre er overmodige og går med kneisende nakke og lar øinene løpe om, går og tripper og klirrer med sine fotringer,
17 Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
skal Herren gjøre Sions døtres isse skurvet, og Herren skal avdekke deres blusel.
18 A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
På den dag skal Herren ta bort de prektige fotringer og soler og halvmåner,
19 ’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
øredobbene og kjedene og slørene,
20 kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
hodeprydelsene og fotkjedene og beltene og lukteflaskene og tryllesmykkene,
21 da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
signetringene og neseringene,
22 tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
høitidsklærne og kåpene og de store tørklær og pungene,
23 da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
speilene og de fine linneter og huene og florslørene.
24 A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
Og det skal skje: I stedet for balsam skal det være stank, og for belte rep, og for kunstig krusede krøller skallet hode, og for vid kappe trang sekk, brennemerke for skjønnhet.
25 Mazanku za su mutu ta wurin takobi, jarumawanku za su mutu a yaƙi.
Dine menn skal falle for sverdet, og dine helter i krigen.
26 Ƙofofin Sihiyona za su yi makoki su kuma yi kuka; za tă zama wofi, za tă zauna a ƙasa.
Og hennes porter klager og sørger, og utplyndret sitter hun på jorden.