< Ishaya 3 >
1 Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,
Voyez, l’Eternel-Cebaot enlève à Jérusalem et à Juda tout appui et tout soutien, toute ressource en pain et toute ressource en eau;
2 jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,
héros et hommes de guerre, juges et prophètes, devins et anciens;
3 shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.
chefs militaires et gens considérés, conseillers ainsi qu’artisans experts et habiles enchanteurs.
4 “Zan sa’yan yara su zama shugabanninsu;’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”
Je leur donnerai des jeunes gens comme maîtres, et des écervelés domineront sur eux.
5 Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.
Chez ce peuple, l’un usera de sévices contre l’autre, chacun contre chacun; le jouvenceau sera arrogant envers le vieillard, l’homme de rien envers le plus respectable.
6 Mutum zai kama ɗaya daga cikin’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”
Que si quelqu’un exerce une pression sur un parent dans la maison paternelle en disant: "Tu possèdes un manteau, consens donc à être notre chef, à soutenir de ta main cet édifice chancelant;"
7 Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”
celui-ci protestera en ce jour par ces paroles: "Non, je ne puis être votre sauveur, alors que, dans ma maison, il n’y a ni pain ni vêtement; ne m’érigez pas en chef de ce peuple"
8 Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.
Oui, Jérusalem a trébuché, Juda est tombé; car leurs paroles et leurs actes sont dirigés contre l’Eternel et bravent ses regards augustes.
9 Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.
L’Impudence de leur visage témoigne contre eux, ils affichent leur crime à l’exemple de Sodome et ne dissimulent rien. Malheur à eux! Ils se sont préparés eux-mêmes la ruine.
10 Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.
Annoncez au juste qu’il sera heureux et jouira du fruit de ses œuvres.
11 Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.
Mais hélas! le malheur atteindra le méchant, car il sera traité selon l’œuvre de ses mains.
12 Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.
Mon peuple, des enfants le pressurent, et des femmes le tyrannisent; ô mon peuple, ce sont tes guides qui t’égarent et qui détruisent la trace de tes routes.
13 Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.
L’Eternel s’avance pour faire justice; il se présente pour juger les peuples;
14 Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.
il vient demander raison aux anciens de son peuple et à ses princes: "C’Est vous qui avez dévoré la vigne, entassé dans vos maisons les dépouilles des pauvres.
15 Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
De quel droit écrasez-vous mon peuple et broyez-vous la face des indigents?" Ainsi parle le Seigneur, l’Eternel-Cebaot.
16 Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
L’Eternel dit encore: "Puisque les filles de Sion sont si arrogantes, s’avançant le cou dressé, lançant des regards provocants, puisqu’elles marchent à pas mesurés et font sonner les clochettes de leurs pieds,
17 Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
le Seigneur dépouillera la tête des filles de Sion et mettra à nu leur honte."
18 A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
En ce jour, le Seigneur supprimera le luxe des clochettes, les filets et les croissants;
19 ’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
les pendants d’oreilles, les bracelets et les voiles;
20 kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
les diadèmes, les chaînettes des pieds, les ceintures, les boîtes à parfums et les amulettes;
21 da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
les bagues et les anneaux du nez;
22 tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
les vêtements de fête, les manteaux, les écharpes et les sachets;
23 da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
les miroirs, les fines tuniques, les turbans et les surtouts…
24 A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
Au lieu de parfums il y aura de la pourriture; au lieu de ceinture, une corde; au lieu de nattes bien tressées, de la calvitie; au lieu d’un large manteau, un cilice; des stigmates de brûlure remplaceront la beauté.
25 Mazanku za su mutu ta wurin takobi, jarumawanku za su mutu a yaƙi.
Tes hommes de guerre tomberont sous le glaive et tes vaillants succomberont dans les combats.
26 Ƙofofin Sihiyona za su yi makoki su kuma yi kuka; za tă zama wofi, za tă zauna a ƙasa.
Une morne tristesse envahira les portes de la ville; Sion, complètement dépouillée, s’assoira à terre.