< Ishaya 3 >

1 Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,
For, lo, the Lord, Jehovah of Hosts, Is turning aside from Jerusalem, And from Judah, stay and staff, Every stay of bread, and every stay of water.
2 jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,
Hero and man of war, judge and prophet, And diviner and elder,
3 shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.
Head of fifty, and accepted of faces, And counsellor, and the wise of artificers, And the intelligent of charmers.
4 “Zan sa’yan yara su zama shugabanninsu;’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”
And I have made youths their heads, And sucklings rule over them.
5 Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.
And the people hath exacted — man upon man, Even a man on his neighbour, Enlarge themselves do the youths against the aged, And the lightly esteemed against the honoured.
6 Mutum zai kama ɗaya daga cikin’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”
When one layeth hold on his brother, [Of] the house of his father, [by] the garment, 'Come, a ruler thou art to us, And this ruin [is] under thy hand.'
7 Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”
He lifteth up, in that day, saying: 'I am not a binder up, And in my house is neither bread nor garment, Ye do not make me a ruler of the people.'
8 Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.
For stumbled hath Jerusalem, and Judah hath fallen, For their tongue and their doings [are] against Jehovah, To provoke the eyes of His glory.
9 Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.
The appearance of their faces witnessed against them, And their sin, as Sodom, they declared, They have not hidden! Woe to their soul, For they have done to themselves evil.
10 Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.
Say ye to the righteous, that [it is] good, Because the fruit of their doings they eat.
11 Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.
Woe to the wicked — evil, Because the deed of his hand is done to him.
12 Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.
My people — its exactors [are] sucklings, And women have ruled over it. My people — thy eulogists are causing to err, And the way of thy paths swallowed up.
13 Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.
Jehovah hath stood up to plead, And He is standing to judge the peoples.
14 Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.
Jehovah into judgment doth enter With elders of His people, and its heads: 'And ye, ye have consumed the vineyard, Plunder of the poor [is] in your houses.
15 Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
What — to you? ye bruise My people, And the faces of the poor ye grind.' An affirmation of the Lord, Jehovah of Hosts, And Jehovah saith:
16 Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
'Because that daughters of Zion have been haughty, And they walk stretching out the neck, And deceiving [with] the eyes, Walking and mincing they go, And with their feet they make a tinkling,
17 Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
The Lord also hath scabbed The crown of the head of daughters of Zion, And Jehovah their simplicity exposeth.
18 A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
In that day doth the Lord turn aside The beauty of the tinkling ornaments, And of the embroidered works, And of the round tires like moons,
19 ’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
Of the drops, and the bracelets, and the mufflers,
20 kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
Of the bonnets, and the ornaments of the legs, And of the bands, And of the perfume boxes, and the amulets,
21 da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
Of the seals, and of the nose-rings,
22 tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
Of the costly apparel, and of the mantles, And of the coverings, and of the purses,
23 da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
Of the mirrors, and of the linen garments, And of the hoods, and of the vails,
24 A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
And it hath been, instead of spice is muck, And instead of a girdle, a rope, And instead of curled work, baldness, And instead of a stomacher a girdle of sackcloth.
25 Mazanku za su mutu ta wurin takobi, jarumawanku za su mutu a yaƙi.
For instead of glory, thy men by sword do fall, And thy might in battle.
26 Ƙofofin Sihiyona za su yi makoki su kuma yi kuka; za tă zama wofi, za tă zauna a ƙasa.
And lamented and mourned have her openings, Yea, she hath been emptied, on the earth she sitteth!

< Ishaya 3 >