< Ishaya 3 >

1 Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,
For behold, the Lord, Jehovah of hosts, Taketh away from Jerusalem and from Judah every stay and support; The whole stay of bread, and the whole stay of water;
2 jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,
The mighty man, and the warrior, The judge, the prophet, the diviner, and the sage,
3 shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.
The captain of fifty, and the honorable man, The counsellor, the expert in arts, and the skilful in charms.
4 “Zan sa’yan yara su zama shugabanninsu;’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”
And I will make boys their princes, And children shall rule over them.
5 Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.
And the people shall oppress one another, Man striving against man, and neighbor against neighbor; The boy shall behave himself insolently toward the aged, And the base toward the honorable.
6 Mutum zai kama ɗaya daga cikin’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”
Then shall a man take hold of his brother in his father's house, [[and say, ]] Thou hast yet clothing, Be thou our ruler, And take this ruin into thy hands!
7 Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”
But in that day shall he lift up his hand, and say: I am no healer; In my house is neither bread nor raiment; Make not me ruler of the people!
8 Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.
For Jerusalem tottereth, and Judah falleth, Because their tongues and their deeds are against Jehovah, To provoke his holy eyes.
9 Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.
Their very countenance witnesseth against them; They publish their sin like Sodom; they hide it not; Woe to them, for they bring evil upon themselves!
10 Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.
Say ye of the righteous that it shall be well with him, For he shall eat the fruit of his doings.
11 Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.
Woe to the wicked, it shall be ill with him, For the work of his hands shall be repaid him!
12 Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.
As for my people, children are their oppressors, And women rule over them. O my people, thy leaders cause thee to err, And destroy the way in which thou walkest!
13 Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.
Jehovah standeth up to maintain his cause; He standeth up to judge his people.
14 Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.
Jehovah entereth into judgment with the elders of his people, and their princes: “So then ye have consumed the vineyard; The plunder of the poor is in your houses!
15 Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
What mean ye, that ye crush my people, And grind the faces of the poor?” Saith Jehovah, the Lord of hosts.
16 Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
Thus, also, saith Jehovah: Because the daughters of Zion are haughty, And walk with outstretched necks, And glance their eyes wantonly, Mincing their steps as they go, And tinkling with their foot-clasps,
17 Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
Therefore will the Lord make their heads bald, And Jehovah will expose their nakedness.
18 A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
In that day shall the Lord take from them The ornaments of the foot-clasps, and the net-works, and the crescents;
19 ’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
The ear-rings, and the bracelets, and the veils;
20 kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
The turbans, and the ankle-chains, and the belts; The perfume-boxes, and the amulets;
21 da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
The finger-rings, and the nose-jewels;
22 tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
The embroidered robes, and the tunics, and the cloaks, and the purses;
23 da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
The mirrors, and the linen shifts, and the head-bands, and the large veils.
24 A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
And instead of perfume there shall be corruption; Instead of a belt, a rope; Instead of curled locks, baldness; Instead of a wide mantle, a covering of sackcloth; Fire-scars instead of beauty.
25 Mazanku za su mutu ta wurin takobi, jarumawanku za su mutu a yaƙi.
Thy men shall fall by the sword, Yea, thy mighty men in battle;
26 Ƙofofin Sihiyona za su yi makoki su kuma yi kuka; za tă zama wofi, za tă zauna a ƙasa.
Her gates shall lament and mourn, And she, being desolate, shall sit upon the ground.

< Ishaya 3 >