< Ishaya 3 >

1 Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,
For lo, the Lord God of hostes will take away from Ierusalem and from Iudah the stay and the strength: euen all the staye of bread, and all the stay of water,
2 jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,
The strong man, and the man of warre, the iudge and the prophet, the prudent and the aged,
3 shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.
The captaine of fiftie, and the honourable, and the counseller, and the cunning artificer, and the eloquent man.
4 “Zan sa’yan yara su zama shugabanninsu;’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”
And I will appoint children to bee their princes, and babes shall rule ouer them.
5 Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.
The people shalbe oppressed one of another, and euery one by his neighbour: the children shall presume against the ancient, and the vile against the honourable.
6 Mutum zai kama ɗaya daga cikin’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”
When euery one shall take holde of his brother of the house of his father, and say, Thou hast clothing: thou shalt bee our prince, and let this fall be vnder thine hand.
7 Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”
In that day hee shall sweare, saying, I cannot bee an helper: for there is no bread in mine house, nor clothing: therefore make me no prince of the people.
8 Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.
Doubtlesse Ierusalem is fallen, and Iudah is fallen downe, because their tongue and workes are against the Lord, to prouoke the eyes of his glory.
9 Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.
The triall of their countenance testifieth against them, yea, they declare their sinnes as Sodom, they hide them not. Wo be vnto their soules: for they haue rewarded euil vnto themselues.
10 Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.
Say ye, Surely it shalbe well with the iust: for they shall eate the fruite of their workes.
11 Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.
Woe be to the wicked, it shalbe euill with him: for the reward of his handes shalbe giuen him.
12 Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.
Children are extortioners of my people, and women haue rule ouer them: O my people, they that leade thee, cause thee to erre, and destroy the way of thy paths.
13 Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.
The Lord standeth vp to pleade, yea, hee standeth to iudge the people.
14 Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.
The Lord shall enter into iudgement with the Ancients of his people and the princes thereof: for ye haue eaten vp the vineyarde: the spoyle of the poore is in your houses.
15 Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
What haue ye to do, that ye beate my people to pieces, and grinde the faces of the poore, saith the Lord, euen the Lord of hoasts?
16 Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
The Lord also saith, Because the daughters of Zion are hautie, and walke with stretched out neckes, and with wandering eyes, walking and minsing as they goe, and making a tinkeling with their feete,
17 Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
Therefore shall the Lord make the heades of the daughters of Zion balde, and the Lord shall discouer their secrete partes.
18 A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
In that day shall the Lord take away the ornament of the slippers, and the calles, and the round tyres,
19 ’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
The sweete balles, and the brasselets, and the bonnets,
20 kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
The tyres of the head, and the sloppes, and the head bandes, and the tablets, and the earings,
21 da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
The rings and the mufflers,
22 tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
The costly apparell and the vailes, and the wimples, and the crisping pinnes,
23 da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
And the glasses and the fine linen, and the hoodes, and the launes.
24 A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
And in steade of sweete sauour, there shall be stinke, and in steade of a girdle, a rent, and in steade of dressing of the heare, baldnesse, and in steade of a stomacher, a girding of sackecloth, and burning in steade of beautie.
25 Mazanku za su mutu ta wurin takobi, jarumawanku za su mutu a yaƙi.
Thy men shall fall by the sworde, and thy strength in the battell.
26 Ƙofofin Sihiyona za su yi makoki su kuma yi kuka; za tă zama wofi, za tă zauna a ƙasa.
Then shall her gates mourne and lament, and she, being desolate, shall sit vpon the ground.

< Ishaya 3 >