< Ishaya 3 >

1 Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,
Gle, Gospod, Jahve nad Vojskama, oduzima Jeruzalemu i Judeji svaku potporu, pomoć u kruhu i pomoć u vodi,
2 jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,
junaka i ratnika, suca i proroka, vrača i starješinu, pedesetnika i odličnika,
3 shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.
savjetnika i mudra gatara i onoga što se bavi čaranjem.
4 “Zan sa’yan yara su zama shugabanninsu;’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”
“A za glavare postavljam im djecu, dajem deranima da njima vladaju.”
5 Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.
Ljudi se glože jedan s drugim i svaki s bližnjim svojim; dijete nasrće na starca, prostak na odličnika
6 Mutum zai kama ɗaya daga cikin’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”
te svatko brata hvata u očinskoj kući: “Ti imaš plašt, budi nam glavarom, uzmi u ruke ovo rasulo!”
7 Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”
A on će se, u dan onaj, braniti: “Neću da budem vidar, nema u mene ni kruha ni plašta: ne stavljajte me narodu za glavara.”
8 Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.
Jeruzalem se ruši i pada Judeja, jer im se jezik i djela Jahvi protive te prkose pogledu Slave njegove.
9 Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.
Lice njihovo protiv njih svjedoči, razmeću se grijehom poput Sodome i ne kriju ga, jao njima, sami sebi propast spremaju.
10 Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.
Kažite: “Blago pravedniku, hranit će se plodom djela svojih!
11 Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.
Jao opakome, zlo će mu biti, na nj će pasti djela ruku njegovih.”
12 Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.
Deran tlači narod moj i žene njime vladaju. O narode moj, vladaoci te tvoji zavode i raskapaju put kojim hodiš.
13 Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.
Ustade Jahve da se popravda s narodom svojim,
14 Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.
Jahve dolazi na sud sa starješinama i glavarima svog naroda: “Vinograd ste moj opustošili, u vašim je kućama što oteste siromahu.
15 Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
S kojim pravom narod moj tlačite i gazite lice siromaha?” - riječ je Jahve, Gospoda nad Vojskama.
16 Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
I reče Jahve: “Što se to ohole kćeri sionske te ispružena vrata hode, okolo okom namiguju, koracima sitnim koracaju, grivnama na nozi zveckaju?
17 Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
Oćelavit će Gospod tjeme kćeri sionskih, obnažit će Jahve golotinju njihovu.”
18 A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
U onaj će dan Gospod strgnuti sve čime se ona ponosi: ukosnice i mjesečiće,
19 ’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
naušnice, narukvice i koprene,
20 kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
poveze, lančiće, pojaseve, bočice s miomirisima i privjese,
21 da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
prstenje i nosne prstenove,
22 tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
skupocjene haljine i plašteve, prijevjese i torbice,
23 da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
zrcala i košuljice, povezače i rupce.
24 A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
Mjesto miomirisa, smrad; mjesto pojasa, konopac; mjesto kovrča, tjeme obrijano; mjesto gizdave halje, kostrijet; mjesto ljepote, žig.
25 Mazanku za su mutu ta wurin takobi, jarumawanku za su mutu a yaƙi.
Muževi tvoji od mača će pasti, junaci tvoji u kreševu.
26 Ƙofofin Sihiyona za su yi makoki su kuma yi kuka; za tă zama wofi, za tă zauna a ƙasa.
Vrata će tvoja kukat' i tugovati, na zemlji ćeš sjedit' napuštena.

< Ishaya 3 >