< Ishaya 29 >

1 Kaitonki, Ariyel, Ariyel birnin da Dawuda ya zauna! Ƙara shekara ga shekara a kuma bar shagulgulanki su yi ta kewayewa.
Ve Ariel, Ariel, du by hvor David slo leir! Legg år til år, la høitidene gå sin rundgang!
2 Duk da haka zan yi wa Ariyel kwanto za tă kuma yi kuka da makoki, za tă zama mini kamar bagaden jini.
Da vil jeg gjøre det trangt for Ariel, og der skal være sorg og jammer; men så skal det bli mig et virkelig Ariel.
3 Zan kafa sansani kewaye da ke duka; zan kewaye ki da hasumiyoyi in tasar miki da ayyukan kwantona na yaƙi.
Jeg vil slå leir rundt omkring dig, og jeg vil kringsette dig med vaktposter og bygge voller mot dig.
4 Za a ƙasƙantar da ke, za ki ƙi yin magana daga ƙasa; maganarki za tă yi ƙasa-ƙasa daga ƙura. Muryarki za tă zama kamar fatalwa daga ƙasa; daga ƙura maganarki zai fito ƙasa-ƙasa.
Da skal du tale lavmælt fra jorden, og fra støvet skal du mumle frem dine ord; og din røst skal lyde fra jorden likesom fra en dødningemaner, og fra støvet skal din tale hviskes.
5 Amma abokan gābanki masu yawa za su zama kamar ƙura mai laushi, sojojinsu masu firgitarwa za su yi ta tashi kamar yayin da iska ta hura. Farat ɗaya, cikin ɗan lokaci,
Men så skal dine fienders mengde bli som fint støv, og voldsmennenes flokk som fykende agner, og det skal skje i et øieblikk, med ett.
6 Ubangiji Maɗaukaki zai zo da tsawa da rawar ƙasa da ƙara mai girma, da hadarin iska da guguwa da harshe na wuta mai ci.
Fra Herren, hærskarenes Gud, skal det komme en hjemsøkelse med bulder og brak og veldige drønn, hvirvelvind og storm og fortærende ildslue.
7 Sa’an nan sojojin dukan al’umman da suka yi yaƙi da Ariyel, da suka fāɗa mata da kagararta suka kuma yi mata kwanto, za su zama kamar yadda yake da mafarki, wahayi da dare,
Og mengden av alle de hedningefolk som strider mot Ariel, skal bli som en drøm, et syn om natten, alle de som strider mot det og dets borg, og som trenger inn på det.
8 kamar sa’ad da mai yunwa yana mafarki cewa yana cin abinci, amma sai ya farka, yunwan tana nan; kamar sa’ad da mai ƙishirwa yana mafarki cewa yana shan ruwa, amma sai ya farka yana suma, da ƙishinsa. Haka zai zama da sojoji na dukan al’ummai da suka yi yaƙi da Dutsen Sihiyona.
Og det skal gå som når den sultne drømmer og synes han eter, men når han våkner, da er han tom, og som når den tørste drømmer og synes han drikker, men når han våkner, se, da er han matt, og hans sjel blir maktløs; således skal det gå alle de mange hedningefolk som strider mot Sions berg.
9 Ku firgita ku kuma yi mamaki, ku makance kanku ku kuma zama a makance; ku bugu, amma ba da ruwan inabi ba, ku yi tangaɗi, amma ba daga barasa ba.
Stirr på hverandre og bli forvirret! Stirr eder blinde, og vær blinde! I er drukne, men ikke av vin; I raver, men ikke av sterk drikk.
10 Ubangiji ya kawo muku barci mai nauyi, Ya rufe idanunku (annabawa); ya rufe kawunanku (masu duba).
For Herren har utøst over eder en dyp søvns ånd, og han har tillukket eders øine, profetene, og tildekket eders hoder, seerne.
11 Gare ku duk wannan wahayi ba kome ba ne sai dai maganganun da aka rufe a cikin littafi. In kuma kun ba da littafin ga wani wanda zai iya karanta, kuka kuma ce masa, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ba zan iya ba; an rufe shi.”
Og således er synet av alt dette blitt eder likesom ordene i en forseglet bok; gir en den til en som skjønner skrift, og sier: Les dette! så sier han: Jeg kan ikke, for den er forseglet.
12 Ko kuwa in kun ba da littafin ga wani wanda ba zai iya karantawa ba, kuka kuma ce, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ban iya karatu ba.”
Eller en rekker boken til en som ikke skjønner skrift, med de ord: Les dette! så sier han: Jeg skjønner ikke skrift.
13 Ubangiji ya ce, “Waɗannan mutane sun zo kusa da ni da bakinsu suka kuma girmama ni da leɓunansu, amma zukatansu suna nesa daga gare ni. Sujadar da suke mini cike take da dokokin da mutane suka koyar.
Og Herren sier: Fordi dette folk holder sig nær til mig med sin munn og ærer mig med sine leber, men holder sitt hjerte langt borte fra mig, og deres frykt for mig er et menneskebud som de har lært,
14 Saboda haka zan firgita waɗannan mutane sau ɗaya da abubuwan banmamaki a kan abubuwan banmamaki; hikimar masu hikima za tă lalace, azancin masu azanci zai ɓace.”
se, derfor vil jeg bli ved å gå underlig frem mot dette folk, underlig og forunderlig, og dets vismenns visdom skal forgå, og dets forstandige menns forstand skal skjule sig.
15 Kaiton waɗanda suke zuwa manyan zurfafa don su ɓoye shirye-shiryensu daga Ubangiji, waɗanda suke aikinsu cikin duhu su yi tunani, “Wa yake ganinmu? Wa zai sani?”
Ve dem som vil skjule i det dype for Herren hvad de har fore, og hvis gjerninger skjer i mørke, og som sier: Hvem ser oss, og hvem kjenner oss?
16 Kuna birkitar abubuwa, sai ka ce an mayar da mai ginin tukwane ya zama yumɓu! Abin da aka yi zai ce wa wanda ya yi shi, “Ba shi ne ya yi ni ba”? Tukunya za tă iya ce wa mai ginin tukwane, “Ba ka san kome ba”?
Hvor forvendte I er! - Er pottemakeren å akte som hans ler, så verket kunde si om ham som gjorde det: Han har ikke gjort mig, og det som er laget, si om ham som laget det: Han skjønner det ikke?
17 Cikin ɗan lokaci, za a mai da Lebanon gona mai taƙi kuma gona mai taƙi za tă zama kamar kurmi?
Ennu bare en liten stund, så skal Libanon bli til fruktbar mark, og den fruktbare mark aktes som skog.
18 A wannan rana kurame za su ji maganganun littafi, daga duruduru da duhu kuma idanun makafi za su gani.
Og på den dag skal de døve høre bokens ord, og ut fra mulm og mørke skal de blindes øine se,
19 Masu tawali’u za su sāke yin farin ciki a cikin Ubangiji; mabukata za su yi farin ciki cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Og de saktmodige skal glede sig enn mere i Herren, og de fattige blandt menneskene skal fryde sig i Israels Hellige;
20 Masu zalunci za su ƙare, masu ba’a za su ɓace, kuma dukan waɗanda suke da ido don mugunta za su hallaka,
for det er forbi med voldsmannen, og det er ute med spotteren, og utryddet blir alle de som er årvåkne til å gjøre urett,
21 waɗanda ta magana kawai sukan mai da mutum mai laifi, waɗanda suke kafa tarko wa mai ba da kāriya a ɗakin shari’a da shaidar ƙarya kuma su hana marar laifi samun shari’ar adalci.
de som gjør et menneske til synder for et ords skyld og legger snarer for den som hevder retten på tinget, og som ved løgn bøier retten for den rettferdige.
22 Saboda haka ga abin da Ubangiji wanda ya fanshi Ibrahim, ya ce wa gidan Yaƙub, “Ba za a ƙara kunyata Yaƙub ba; fuskokinsu kuma ba za su ƙara yanƙwanewa ba.
Derfor sier Herren så til Jakobs hus, Herren som forløste Abraham: Nu skal Jakob ikke bli til skamme, og nu skal hans åsyn ikke blekne;
23 Sa’ad da suka ga’ya’yansu a tsakiyarsu, aikin hannuwansu, za su kiyaye sunana da tsarki; za su san tsarkin Mai Tsarkin nan na Yaƙub, za su kuma ji tsoron Allah na Isra’ila.
for når han og hans barn ser mine henders gjerning i sin midte, så skal de hellige mitt navn, og de skal hellige Jakobs Hellige, og Israels Gud skal de frykte.
24 Su da suke marasa azanci a ruhu za su sami fahimtar; waɗanda suke gunaguni za su yarda da koyarwa.”
Og de hvis ånd fór vill, skal lære forstand, og de knurrende skal ta imot lærdom.

< Ishaya 29 >