< Ishaya 29 >
1 Kaitonki, Ariyel, Ariyel birnin da Dawuda ya zauna! Ƙara shekara ga shekara a kuma bar shagulgulanki su yi ta kewayewa.
Voi Arielia, Arielia, kaupunkia, jonne Daavid asetti leirinsä! Liittäkää vuosi vuoteen, kiertäkööt juhlat kiertonsa,
2 Duk da haka zan yi wa Ariyel kwanto za tă kuma yi kuka da makoki, za tă zama mini kamar bagaden jini.
niin minä ahdistan Arielia, ja se on oleva täynnä valitusta ja vaikerrusta, oleva minulle kuin Jumalan uhriliesi.
3 Zan kafa sansani kewaye da ke duka; zan kewaye ki da hasumiyoyi in tasar miki da ayyukan kwantona na yaƙi.
Minä asetan leirini yltympäri sinua vastaan ja saarran sinut vartiostoilla ja luon vallit sinua vastaan.
4 Za a ƙasƙantar da ke, za ki ƙi yin magana daga ƙasa; maganarki za tă yi ƙasa-ƙasa daga ƙura. Muryarki za tă zama kamar fatalwa daga ƙasa; daga ƙura maganarki zai fito ƙasa-ƙasa.
Silloin sinä puhut maasta matalalta, sanasi tulevat vaimeina tomusta, sinä uikutat kuin vainajahenki maasta, puheesi tulee supisten tomusta.
5 Amma abokan gābanki masu yawa za su zama kamar ƙura mai laushi, sojojinsu masu firgitarwa za su yi ta tashi kamar yayin da iska ta hura. Farat ɗaya, cikin ɗan lokaci,
Mutta sinun vainolaistesi lauma on oleva niinkuin hieno pöly, ja väkivaltaisten lauma niinkuin lentävät akanat, ja tämä tapahtuu äkkiä, silmänräpäyksessä:
6 Ubangiji Maɗaukaki zai zo da tsawa da rawar ƙasa da ƙara mai girma, da hadarin iska da guguwa da harshe na wuta mai ci.
Herra Sebaot etsiskelee sinua ukkosenjylinässä ja maanjäristyksessä, kovassa pauhinassa, myrskyssä ja rajuilmassa, kuluttavan tulen liekissä.
7 Sa’an nan sojojin dukan al’umman da suka yi yaƙi da Ariyel, da suka fāɗa mata da kagararta suka kuma yi mata kwanto, za su zama kamar yadda yake da mafarki, wahayi da dare,
Niinkuin yöllinen uninäky on oleva kansain lauma, joka sotii Arielia vastaan, kaikki, jotka sotivat sitä ja sen varustuksia vastaan ja sitä ahdistavat.
8 kamar sa’ad da mai yunwa yana mafarki cewa yana cin abinci, amma sai ya farka, yunwan tana nan; kamar sa’ad da mai ƙishirwa yana mafarki cewa yana shan ruwa, amma sai ya farka yana suma, da ƙishinsa. Haka zai zama da sojoji na dukan al’ummai da suka yi yaƙi da Dutsen Sihiyona.
Niinkuin nälkäinen on unissaan syövinänsä, mutta herää hiuka sydämessä, ja niinkuin janoinen on unissaan juovinansa, mutta herää, ja katso, hän on nääntynyt ja himoitsee juoda, niin on oleva kaikki kansain lauma, joka sotii Siionin vuorta vastaan.
9 Ku firgita ku kuma yi mamaki, ku makance kanku ku kuma zama a makance; ku bugu, amma ba da ruwan inabi ba, ku yi tangaɗi, amma ba daga barasa ba.
Hämmästykää ja ihmetelkää, tuijottakaa sokeiksi itsenne ja sokeiksi jääkää! He ovat juovuksissa, vaikkeivät viinistä, hoipertelevat, vaikkeivät väkijuomasta.
10 Ubangiji ya kawo muku barci mai nauyi, Ya rufe idanunku (annabawa); ya rufe kawunanku (masu duba).
Sillä Herra on vuodattanut teidän päällenne raskaan unen hengen ja sulkenut teidän silmänne-profeettanne, ja peittänyt teidän päänne-näkijänne.
11 Gare ku duk wannan wahayi ba kome ba ne sai dai maganganun da aka rufe a cikin littafi. In kuma kun ba da littafin ga wani wanda zai iya karanta, kuka kuma ce masa, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ba zan iya ba; an rufe shi.”
Niin on kaikki ilmoitus teille niinkuin lukitun kirjan sanat; jos se annetaan kirjantaitavalle ja sanotaan: "Lue tämä", niin hän vastaa: "Ei voi, sillä se on lukittu",
12 Ko kuwa in kun ba da littafin ga wani wanda ba zai iya karantawa ba, kuka kuma ce, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ban iya karatu ba.”
ja jos kirja annetaan kirjantaitamattomalle ja sanotaan: "Lue tämä", niin hän vastaa: "En osaa lukea".
13 Ubangiji ya ce, “Waɗannan mutane sun zo kusa da ni da bakinsu suka kuma girmama ni da leɓunansu, amma zukatansu suna nesa daga gare ni. Sujadar da suke mini cike take da dokokin da mutane suka koyar.
Ja Herra sanoi: Koska tämä kansa lähestyy minua suullaan ja kunnioittaa minua huulillaan, mutta pitää sydämensä minusta kaukana, ja koska heidän jumalanpelkonsa on vain opittuja ihmiskäskyjä,
14 Saboda haka zan firgita waɗannan mutane sau ɗaya da abubuwan banmamaki a kan abubuwan banmamaki; hikimar masu hikima za tă lalace, azancin masu azanci zai ɓace.”
sentähden, katso, minä vielä teen tälle kansalle kummia tekoja-kummia ja ihmeitä, ja sen viisaitten viisaus häviää, ja sen ymmärtäväisten ymmärrys katoaa.
15 Kaiton waɗanda suke zuwa manyan zurfafa don su ɓoye shirye-shiryensu daga Ubangiji, waɗanda suke aikinsu cikin duhu su yi tunani, “Wa yake ganinmu? Wa zai sani?”
Voi niitä, jotka syvälle kätkevät hankkeensa Herralta, joiden teot tapahtuvat pimeässä ja jotka sanovat: "Kuka meitä näkee, kuka meistä tietää?"
16 Kuna birkitar abubuwa, sai ka ce an mayar da mai ginin tukwane ya zama yumɓu! Abin da aka yi zai ce wa wanda ya yi shi, “Ba shi ne ya yi ni ba”? Tukunya za tă iya ce wa mai ginin tukwane, “Ba ka san kome ba”?
Voi mielettömyyttänne! Onko savi savenvalajan veroinen? Ja sanooko työ tekijästään: "Ei hän ole minua tehnyt", tai sanooko kuva kuvaajastaan: "Ei hän mitään ymmärrä"?
17 Cikin ɗan lokaci, za a mai da Lebanon gona mai taƙi kuma gona mai taƙi za tă zama kamar kurmi?
Vain lyhyt hetki enää, niin Libanon muuttuu puutarhaksi, ja puutarha on metsän veroinen.
18 A wannan rana kurame za su ji maganganun littafi, daga duruduru da duhu kuma idanun makafi za su gani.
Sinä päivänä kuurot kuulevat kirjan sanat, ja sokeiden silmät näkevät vapaina synkeästä pimeydestä.
19 Masu tawali’u za su sāke yin farin ciki a cikin Ubangiji; mabukata za su yi farin ciki cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Nöyrät saavat yhä uutta iloa Herrassa, ja ihmisistä köyhimmätkin riemuitsevat Israelin Pyhästä.
20 Masu zalunci za su ƙare, masu ba’a za su ɓace, kuma dukan waɗanda suke da ido don mugunta za su hallaka,
Sillä väkivaltaisista on tullut loppu, pilkkaajat ovat hävinneet, ja kaikki vääryyteen valppaat ovat tuhotut,
21 waɗanda ta magana kawai sukan mai da mutum mai laifi, waɗanda suke kafa tarko wa mai ba da kāriya a ɗakin shari’a da shaidar ƙarya kuma su hana marar laifi samun shari’ar adalci.
ne, jotka sanallansa langettavat ihmisiä syyhyn ja virittävät pauloja sille, joka oikeutta puolustaa portissa, ja verukkeilla syyttömän asian vääräksi vääntävät.
22 Saboda haka ga abin da Ubangiji wanda ya fanshi Ibrahim, ya ce wa gidan Yaƙub, “Ba za a ƙara kunyata Yaƙub ba; fuskokinsu kuma ba za su ƙara yanƙwanewa ba.
Sentähden Herra, joka Aabrahamin vapahti, sanoo Jaakobin heimolle näin: Ei Jaakob enää joudu häpeään, eivätkä hänen kasvonsa enää kalpene.
23 Sa’ad da suka ga’ya’yansu a tsakiyarsu, aikin hannuwansu, za su kiyaye sunana da tsarki; za su san tsarkin Mai Tsarkin nan na Yaƙub, za su kuma ji tsoron Allah na Isra’ila.
Sillä kun hän näkee, kun hänen lapsensa näkevät keskellänsä minun kätteni työn, niin he pyhittävät minun nimeni, pitävät pyhänä Jaakobin Pyhän ja peljästyvät Israelin Jumalaa.
24 Su da suke marasa azanci a ruhu za su sami fahimtar; waɗanda suke gunaguni za su yarda da koyarwa.”
Ja hengessään eksyväiset käsittävät ymmärryksen, ja napisevaiset ottavat oppia.