< Ishaya 29 >
1 Kaitonki, Ariyel, Ariyel birnin da Dawuda ya zauna! Ƙara shekara ga shekara a kuma bar shagulgulanki su yi ta kewayewa.
Woe [to] Ariel, Ariel, The city of the encampment of David! Add year to year, let festivals go around.
2 Duk da haka zan yi wa Ariyel kwanto za tă kuma yi kuka da makoki, za tă zama mini kamar bagaden jini.
And I have sent distress to Ariel, And it has been lamentation and mourning, And it has been to me as Ariel.
3 Zan kafa sansani kewaye da ke duka; zan kewaye ki da hasumiyoyi in tasar miki da ayyukan kwantona na yaƙi.
And I encamped, O babbler, against you, And I laid siege against you—a camp. And I raised up bulwarks against you.
4 Za a ƙasƙantar da ke, za ki ƙi yin magana daga ƙasa; maganarki za tă yi ƙasa-ƙasa daga ƙura. Muryarki za tă zama kamar fatalwa daga ƙasa; daga ƙura maganarki zai fito ƙasa-ƙasa.
And you have been low, You speak from the earth, And make your saying low from the dust, And your voice has been from the earth, As one having a familiar spirit, And your saying whispers from the dust,
5 Amma abokan gābanki masu yawa za su zama kamar ƙura mai laushi, sojojinsu masu firgitarwa za su yi ta tashi kamar yayin da iska ta hura. Farat ɗaya, cikin ɗan lokaci,
And as small dust has been The multitude of those scattering you, And as chaff passing on the multitude of the terrible, And it has been in an instant—suddenly.
6 Ubangiji Maɗaukaki zai zo da tsawa da rawar ƙasa da ƙara mai girma, da hadarin iska da guguwa da harshe na wuta mai ci.
You are inspected by YHWH of Hosts, With thunder, and with an earthquake, And great noise, windstorm, and whirlwind, And flame of devouring fire.
7 Sa’an nan sojojin dukan al’umman da suka yi yaƙi da Ariyel, da suka fāɗa mata da kagararta suka kuma yi mata kwanto, za su zama kamar yadda yake da mafarki, wahayi da dare,
And as a dream, a vision of night, Has been the multitude of all the nations Who are warring against Ariel, And all its warriors, and its bulwark, Even of those distressing her.
8 kamar sa’ad da mai yunwa yana mafarki cewa yana cin abinci, amma sai ya farka, yunwan tana nan; kamar sa’ad da mai ƙishirwa yana mafarki cewa yana shan ruwa, amma sai ya farka yana suma, da ƙishinsa. Haka zai zama da sojoji na dukan al’ummai da suka yi yaƙi da Dutsen Sihiyona.
And it has been, as when the hungry dreams, And behold, he is eating, And he has awoken, And his soul [is] empty, And as when the thirsty dreams, And behold, he is drinking, And he has awoken, And behold, he is weary, And his soul is longing, So is the multitude of all the nations Who are warring against Mount Zion.
9 Ku firgita ku kuma yi mamaki, ku makance kanku ku kuma zama a makance; ku bugu, amma ba da ruwan inabi ba, ku yi tangaɗi, amma ba daga barasa ba.
Linger and wonder, look, indeed, look, Be drunk, and not with wine, Stagger, and not with strong drink.
10 Ubangiji ya kawo muku barci mai nauyi, Ya rufe idanunku (annabawa); ya rufe kawunanku (masu duba).
For YHWH has poured out a spirit of deep sleep on you, And He closes your eyes—the prophets, And your heads—the seers—He covered.
11 Gare ku duk wannan wahayi ba kome ba ne sai dai maganganun da aka rufe a cikin littafi. In kuma kun ba da littafin ga wani wanda zai iya karanta, kuka kuma ce masa, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ba zan iya ba; an rufe shi.”
And the vision of the whole is to you, As words of the sealed scroll, That they give to one knowing scrolls, Saying, “Please read this,” And he has said, “I am not able, for it [is] sealed”;
12 Ko kuwa in kun ba da littafin ga wani wanda ba zai iya karantawa ba, kuka kuma ce, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ban iya karatu ba.”
And the scroll is given to him who has not known scrolls, Saying, “Please read this,” And he has said, “I have not known scrolls.”
13 Ubangiji ya ce, “Waɗannan mutane sun zo kusa da ni da bakinsu suka kuma girmama ni da leɓunansu, amma zukatansu suna nesa daga gare ni. Sujadar da suke mini cike take da dokokin da mutane suka koyar.
And the Lord says: “Because this people has drawn near with its mouth, And they have honored Me with its lips, And it has put its heart far off from Me, And their fear of Me is a precept taught by men!
14 Saboda haka zan firgita waɗannan mutane sau ɗaya da abubuwan banmamaki a kan abubuwan banmamaki; hikimar masu hikima za tă lalace, azancin masu azanci zai ɓace.”
Therefore, behold, I am adding to do wonderfully with this people, A wonder, and a marvel, And the wisdom of its wise ones has perished, And the understanding of its intelligent ones hides itself.”
15 Kaiton waɗanda suke zuwa manyan zurfafa don su ɓoye shirye-shiryensu daga Ubangiji, waɗanda suke aikinsu cikin duhu su yi tunani, “Wa yake ganinmu? Wa zai sani?”
Woe [to] those going deep from YHWH to hide counsel, And whose works have been in darkness. And they say, “Who is seeing us? And who is knowing us?”
16 Kuna birkitar abubuwa, sai ka ce an mayar da mai ginin tukwane ya zama yumɓu! Abin da aka yi zai ce wa wanda ya yi shi, “Ba shi ne ya yi ni ba”? Tukunya za tă iya ce wa mai ginin tukwane, “Ba ka san kome ba”?
Your perversion! Is the potter esteemed as clay, That the work says of its maker, “He has not made me?” And the framed thing said of its framer, “He did not understand?”
17 Cikin ɗan lokaci, za a mai da Lebanon gona mai taƙi kuma gona mai taƙi za tă zama kamar kurmi?
Is it not yet a very little [while], And Lebanon has turned into a fruitful field, And the fruitful field is reckoned for a forest?
18 A wannan rana kurame za su ji maganganun littafi, daga duruduru da duhu kuma idanun makafi za su gani.
And the deaf have heard the words of a scroll in that day, And out of thick darkness, and out of darkness, The eyes of the blind see.
19 Masu tawali’u za su sāke yin farin ciki a cikin Ubangiji; mabukata za su yi farin ciki cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
And the humble have added joy in YHWH, And the poor among men Rejoice in the Holy One of Israel.
20 Masu zalunci za su ƙare, masu ba’a za su ɓace, kuma dukan waɗanda suke da ido don mugunta za su hallaka,
For the terrible one has ceased, And the scorner has been consumed, And all watching for iniquity have been cut off,
21 waɗanda ta magana kawai sukan mai da mutum mai laifi, waɗanda suke kafa tarko wa mai ba da kāriya a ɗakin shari’a da shaidar ƙarya kuma su hana marar laifi samun shari’ar adalci.
Who cause men to sin in word, And lay a snare for a reprover in the gate, And turn aside the righteous into emptiness.
22 Saboda haka ga abin da Ubangiji wanda ya fanshi Ibrahim, ya ce wa gidan Yaƙub, “Ba za a ƙara kunyata Yaƙub ba; fuskokinsu kuma ba za su ƙara yanƙwanewa ba.
Therefore, thus said YHWH, Who ransomed Abraham, Concerning the house of Jacob: “Jacob is not ashamed now, Nor does his face now become pale,
23 Sa’ad da suka ga’ya’yansu a tsakiyarsu, aikin hannuwansu, za su kiyaye sunana da tsarki; za su san tsarkin Mai Tsarkin nan na Yaƙub, za su kuma ji tsoron Allah na Isra’ila.
For in his seeing his children, The work of My hand, in his midst, They sanctify My Name, And have sanctified the Holy One of Jacob, And they declare the God of Israel fearful.
24 Su da suke marasa azanci a ruhu za su sami fahimtar; waɗanda suke gunaguni za su yarda da koyarwa.”
And the erring in spirit have known understanding, And murmurers learn doctrine!”