< Ishaya 29 >

1 Kaitonki, Ariyel, Ariyel birnin da Dawuda ya zauna! Ƙara shekara ga shekara a kuma bar shagulgulanki su yi ta kewayewa.
Ah, Ariel, Ariel, the city where David encamped! Add ye year to year, let the feasts come round!
2 Duk da haka zan yi wa Ariyel kwanto za tă kuma yi kuka da makoki, za tă zama mini kamar bagaden jini.
Then will I distress Ariel, and there shall be mourning and moaning; and she shall be unto Me as a hearth of God.
3 Zan kafa sansani kewaye da ke duka; zan kewaye ki da hasumiyoyi in tasar miki da ayyukan kwantona na yaƙi.
And I will encamp against thee round about, and will lay siege against thee with a mound, and I will raise siege works against thee.
4 Za a ƙasƙantar da ke, za ki ƙi yin magana daga ƙasa; maganarki za tă yi ƙasa-ƙasa daga ƙura. Muryarki za tă zama kamar fatalwa daga ƙasa; daga ƙura maganarki zai fito ƙasa-ƙasa.
And brought down thou shalt speak out of the ground, and thy speech shall be low out of the dust; and thy voice shall be as of a ghost out of the ground, and thy speech shall chirp out of the dust.
5 Amma abokan gābanki masu yawa za su zama kamar ƙura mai laushi, sojojinsu masu firgitarwa za su yi ta tashi kamar yayin da iska ta hura. Farat ɗaya, cikin ɗan lokaci,
But the multitude of thy foes shall be like small dust, and the multitude of the terrible ones as chaff that passeth away; yea, it shall be at an instant suddenly —
6 Ubangiji Maɗaukaki zai zo da tsawa da rawar ƙasa da ƙara mai girma, da hadarin iska da guguwa da harshe na wuta mai ci.
There shall be a visitation from the LORD of hosts with thunder, and with earthquake, and great noise, with whirlwind and tempest, and the flame of a devouring fire.
7 Sa’an nan sojojin dukan al’umman da suka yi yaƙi da Ariyel, da suka fāɗa mata da kagararta suka kuma yi mata kwanto, za su zama kamar yadda yake da mafarki, wahayi da dare,
And the multitude of all the nations that war against Ariel, even all that war against her, and the bulwarks about her, and they that distress her, shall be as a dream, a vision of the night.
8 kamar sa’ad da mai yunwa yana mafarki cewa yana cin abinci, amma sai ya farka, yunwan tana nan; kamar sa’ad da mai ƙishirwa yana mafarki cewa yana shan ruwa, amma sai ya farka yana suma, da ƙishinsa. Haka zai zama da sojoji na dukan al’ummai da suka yi yaƙi da Dutsen Sihiyona.
And it shall be as when a hungry man dreameth, and, behold, he eateth, but he awaketh, and his soul is empty; or as when a thirsty man dreameth, and, behold, he drinketh, but he awaketh, and, behold, he is faint, and his soul hath appetite — so shall the multitude of all the nations be, that fight against mount Zion.
9 Ku firgita ku kuma yi mamaki, ku makance kanku ku kuma zama a makance; ku bugu, amma ba da ruwan inabi ba, ku yi tangaɗi, amma ba daga barasa ba.
Stupefy yourselves, and be stupid! Blind yourselves, and be blind! ye that are drunken, but not with wine, that stagger, but not with strong drink.
10 Ubangiji ya kawo muku barci mai nauyi, Ya rufe idanunku (annabawa); ya rufe kawunanku (masu duba).
For the LORD hath poured out upon you the spirit of deep sleep, and hath closed your eyes; the prophets, and your heads, the seers, hath He covered.
11 Gare ku duk wannan wahayi ba kome ba ne sai dai maganganun da aka rufe a cikin littafi. In kuma kun ba da littafin ga wani wanda zai iya karanta, kuka kuma ce masa, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ba zan iya ba; an rufe shi.”
And the vision of all this is become unto you as the words of a writing that is sealed, which men deliver to one that is learned, saying: 'Read this, I pray thee'; and he saith: 'I cannot, for it is sealed';
12 Ko kuwa in kun ba da littafin ga wani wanda ba zai iya karantawa ba, kuka kuma ce, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ban iya karatu ba.”
and the writing is delivered to him that is not learned, saying: 'Read this, I pray thee'; and he saith: 'I am not learned.'
13 Ubangiji ya ce, “Waɗannan mutane sun zo kusa da ni da bakinsu suka kuma girmama ni da leɓunansu, amma zukatansu suna nesa daga gare ni. Sujadar da suke mini cike take da dokokin da mutane suka koyar.
And the Lord said: Forasmuch as this people draw near, and with their mouth and with their lips do honour Me, but have removed their heart far from Me, and their fear of Me is a commandment of men learned by rote;
14 Saboda haka zan firgita waɗannan mutane sau ɗaya da abubuwan banmamaki a kan abubuwan banmamaki; hikimar masu hikima za tă lalace, azancin masu azanci zai ɓace.”
Therefore, behold, I will again do a marvellous work among this people, even a marvellous work and a wonder; and the wisdom of their wise men shall perish, and the prudence of their prudent men shall be hid.
15 Kaiton waɗanda suke zuwa manyan zurfafa don su ɓoye shirye-shiryensu daga Ubangiji, waɗanda suke aikinsu cikin duhu su yi tunani, “Wa yake ganinmu? Wa zai sani?”
Woe unto them that seek deep to hide their counsel from the LORD, and their works are in the dark, and they say: 'Who seeth us? and who knoweth us?'
16 Kuna birkitar abubuwa, sai ka ce an mayar da mai ginin tukwane ya zama yumɓu! Abin da aka yi zai ce wa wanda ya yi shi, “Ba shi ne ya yi ni ba”? Tukunya za tă iya ce wa mai ginin tukwane, “Ba ka san kome ba”?
O your perversity! Shall the potter be esteemed as clay; that the thing made should say of him that made it: 'He made me not'; or the thing framed say of him that framed it: 'He hath no understanding?'
17 Cikin ɗan lokaci, za a mai da Lebanon gona mai taƙi kuma gona mai taƙi za tă zama kamar kurmi?
Is it not yet a very little while, and Lebanon shall be turned into a fruitful field, and the fruitful field shall be esteemed as a forest?
18 A wannan rana kurame za su ji maganganun littafi, daga duruduru da duhu kuma idanun makafi za su gani.
And in that day shall the deaf hear the words of a book, and the eyes of the blind shall see out of obscurity and out of darkness.
19 Masu tawali’u za su sāke yin farin ciki a cikin Ubangiji; mabukata za su yi farin ciki cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
The humble also shall increase their joy in the LORD, and the neediest among men shall exult in the Holy One of Israel.
20 Masu zalunci za su ƙare, masu ba’a za su ɓace, kuma dukan waɗanda suke da ido don mugunta za su hallaka,
For the terrible one is brought to nought, and the scorner ceaseth, and all they that watch for iniquity are cut off;
21 waɗanda ta magana kawai sukan mai da mutum mai laifi, waɗanda suke kafa tarko wa mai ba da kāriya a ɗakin shari’a da shaidar ƙarya kuma su hana marar laifi samun shari’ar adalci.
That make a man an offender by words, and lay a snare for him that reproveth in the gate, and turn aside the just with a thing of nought.
22 Saboda haka ga abin da Ubangiji wanda ya fanshi Ibrahim, ya ce wa gidan Yaƙub, “Ba za a ƙara kunyata Yaƙub ba; fuskokinsu kuma ba za su ƙara yanƙwanewa ba.
Therefore thus saith the LORD, who redeemed Abraham, concerning the house of Jacob: Jacob shall not now be ashamed, neither shall his face now wax pale;
23 Sa’ad da suka ga’ya’yansu a tsakiyarsu, aikin hannuwansu, za su kiyaye sunana da tsarki; za su san tsarkin Mai Tsarkin nan na Yaƙub, za su kuma ji tsoron Allah na Isra’ila.
When he seeth his children, the work of My hands, in the midst of him, that they sanctify My name; yea, they shall sanctify the Holy One of Jacob, and shall stand in awe of the God of Israel.
24 Su da suke marasa azanci a ruhu za su sami fahimtar; waɗanda suke gunaguni za su yarda da koyarwa.”
They also that err in spirit shall come to understanding, and they that murmur shall learn instruction.

< Ishaya 29 >