< Ishaya 28 >

1 Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
Горе тобі, Самарії, короні пишно́ти Єфре́млян п'яни́х, квітці зів'ялій краси́ його го́рдости, що лежить на верхі́в'ї долини врожа́йної, від вина поп'яні́лих!
2 Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
Ось поту́жний та сильний у Господа, — мов злива із градом, мов буря руїнна, мов по́відь сильна́, заливна́, його кине на землю із силою!
3 Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
Ногами пото́птана буде корона пишно́ти Єфре́млян п'яни́х,
4 Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
і станеться квітка зів'я́ла краси́ його гордости, що на верхі́в'ї долини врожайної, немов передчасно дозріла та смо́ква, що її як побачить люди́на, ковтає її, як вона ще в долоні його!
5 A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
Стане Господь Саваот того дня за прекрасну корону, і за пишний вінок для останку наро́ду Його,
6 Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
і духом права тому́, хто сидить у суді, і хоробрістю тим, хто до брами пове́ртає бій!
7 Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
І ось ці від вина позбива́лись з дороги, і від п'янко́го напо́ю хитаються: священик і пророк позбива́лись з дороги напо́єм п'янки́м, від вина збаламу́тились, від напо́ю п'янко́го хита́ються, блу́дять вони у видіннях, у постановах своїх спотика́ються.
8 Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
Бо всі столи повні блюво́тою калу, аж місця нема!
9 “Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
„Кого буде навчати пізна́ння, і кому́ виясняти об'я́влення буде? Відставлених від молока чи від перс повідлу́чуваних?
10 Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
Бо на заповідь заповідь, заповідь на заповідь, пра́вило на пра́вило, пра́вило на пра́вило, трохи тут, трохи там“.
11 To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
Тому незрозумілими у́стами й іншою мовою буде казати наро́дові цьому
12 waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
Отой, Хто до них говорив: „Це спочи́нок! Дайте змученому відпочи́ти, — і це відпочинок“, — та вони не хотіли послухати.
13 Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
І станеться їм слово Господа: заповідь на заповідь, заповідь на заповідь, пра́вило на пра́вило, правило на правило, трохи тут, трохи там, щоб пішли та попадали на́взнак, і щоб були зла́мані й впали до па́стки й злови́лися!
14 Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
Тому то послухайте слова Господнього, ганьби́телі, що пануєте над тим наро́дом, що в Єфусалимі!
15 Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol h7585)
Бо кажете ви: „Заповіта ми склали зо смертю і з шео́лом зробили умову. Як перейде той бич, мов вода заливна́, то не при́йде до нас, бо брехню́ ми зробили притулком своїм, і в брехні́ ми схова́лись!“ (Sheol h7585)
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
Тому́ Господь Бог сказав так: Оце поклав каменя Я на Сіоні, каменя ви́пробуваного, нарі́жного, дорогого, міцно закла́деного. Хто вірує в нього, не буде той засоро́млений!
17 Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
І право за міри́ло Я покладу́, а справедливість — вагою; і приту́лок брехні́ град понищить, а схо́вище во́ди заллють!
18 Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol h7585)
І заповіт ваш із смертю пола́маний буде, а ваша умова з шео́лом не втри́мається: як пере́йде нищівна́ ка́ра, то вас вона сто́пче! (Sheol h7585)
19 A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
Коли тільки пере́йде вона, вона вас забере, бо щора́нку вона перехо́дити буде, удень та вночі, — і ста́неться, — тільки з тремтінням ви бу́дете слу́хати звістку про це.
20 wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
Бо буде постеля коротка, щоб на ній розтягну́тись, а покрива́ло вузьке, щоб накри́тися ним,
21 Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
Бо повстане Господь, немов на горі Перацім; затремтить Він у гніві, немов у долині в Гів'оні, щоб Свій чин учинити, предивний Свій чин, щоб зробити роботу Свою, незви́чайну роботу Свою!
22 Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
Тож не насміха́йтесь тепер, щоб не стали міцнішими ваші кайда́ни, бо призна́чене зни́щення чув я від Господа, Бога Саваота, про всю землю.
23 Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
Візьміть це до ушей і почуйте мій голос, послухайте пильно й почуйте мій голос!
24 Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
Чи кожного дня о́ре ра́тай на по́сів, ралить землю свою й борону́є?
25 Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
Чи ж, як рівною зробить поверхню її, він не сіє чорну́ху й не кидає кмин, не розсіва́є пшеницю та просо й ячмінь на озна́ченім місці, а жито в ме́жах її?
26 Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
І за правом напу́тив його, його Бог його ви́вчив цього́:
27 Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
Бож не бороно́ю чорну́ха молотиться, і ко́ло возо́ве не ходить по кмині, а палицею б'ють чорну́ху та києм — той кмин.
28 Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
Розтирається збіжжя? Ні, бо його не наза́вжди моло́титься ко́нче, і підганяють ко́ло возо́ве та коні на нього, а не розтирають його.
29 Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.
І це вийшло від Господа Саваота, — чудова порада Його, і велика премудрість Його!

< Ishaya 28 >