< Ishaya 28 >
1 Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
¡Ay! Corona de orgullo de los ebrios de Efraín, y la flor marchita de su gloria que está sobre la cabeza de los vencidos por él vino.
2 Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
Mira, el Señor tiene un hombre fuerte y poderoso; Como una lluvia de granizo, una tormenta de destrucción, como el desbordamiento de un río fuerte, los vencerá violentamente.
3 Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
La corona de orgullo de los que se entregan al vino en Efraín será aplastada bajo el pie;
4 Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
Y la flor marchita él adorno de su gloria, que está en la cabeza del valle fértil, será como el primer fruto temprano antes del verano; que un hombre toma y pone en su boca en el momento en que lo ve.
5 A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
En aquel día, el Señor de los ejércitos será una corona de gloria y un hermoso adorno para el resto de su pueblo;
6 Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
Y un espíritu de sabiduría para el juez, y fortaleza para los que rechazan a los atacantes en la puerta de la ciudad.
7 Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
Y además, estos se tambalean por él vino, y han salido del camino correcto a través de una bebida fuerte: el sacerdote y el profeta se tambalean por la bebida fuerte, son vencidos por el vino, han salido del camino a través de bebida fuerte; Su visión es falsa, se equivocan en sus decisiones.
8 Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
Porque todas las mesas están cubiertas de vómito asqueroso, y no hay un lugar limpio.
9 “Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
¿A quién dará conocimiento? ¿Y a quién hará entender el mensaje? ¿Será para aquellos que han dejado de tomar leche y son como niños chiquitos?
10 Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
Porque es una regla tras otra; una línea tras otra, Aquí un poco, Allí un poco.
11 To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
No, pero con palabras raras y con una lengua extraña, dará su palabra a este pueblo:
12 waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
A quien dijo: Este es el reposo, dale descanso al cansado; y por esto puedes obtener nueva fuerza; pero ellos no quisieron oír.
13 Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
Por esta causa, la palabra del Señor será para ellos regla tras regla, línea tras línea, aquí un poco, allí un poco; para que puedan seguir su camino, y al retroceder, sean quebrantados, enlazados y presos.
14 Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
Escuchen, pues, la palabra del Señor, hombres de orgullo, gobernantes de este pueblo en Jerusalén.
15 Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol )
Porque han dicho: Hemos hecho de la muerte nuestro amigo, y con el inframundo hemos llegado a un acuerdo; cuando las aguas desbordantes pasen, no se acercarán a nosotros; porque estamos buscando la mentira por nuestro refugio, y en él engaño nos hemos escondido. (Sheol )
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
Por esta causa dice el Señor Dios: Mira, estoy colocando en Sión como una base, una piedra, una piedra escogida, una piedra angular de cimiento firme y de gran valor, y el que crea no se apresure.
17 Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
Tomaré la decisión correcta, la línea de medición, y la justicia, el peso. Y la tormenta de hielo destruirá el lugar de refugio de las mentiras, y el lugar de protección será arrasado por las aguas que fluyen.
18 Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol )
Y tu pacto con la muerte, será anulado, y tu acuerdo con el inframundo se romperá; cuando pase el azote abrumador, serán pisoteados por él. (Sheol )
19 A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
Cuantas veces pase, los alcanzará; porque vendrán mañana tras mañana, día y noche, y será por espanto él solo entender el reporte.
20 wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
Porque la cama no es lo suficientemente larga para que un hombre se estire, y la cubierta no es lo suficientemente ancha como para cubrirse.
21 Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
Porque el SEÑOR subirá como en el monte Perazim, será llevado a la ira como en el valle de Gabaón; para que pueda hacer su obra, su extraña obra; y dar efecto a su acto, su acto extraordinario.
22 Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
Y ahora, cuídate de no burlarte de él, o tus cadenas se harán fuertes; porque he recibido una palabra del Señor, el Señor de los ejércitos, de un fin, de un final completo, que ha de venir a toda la tierra.
23 Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
Sean tus oídos abiertos a mi voz; Pon atención a lo que digo.
24 Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
¿Está el arado para arar siempre? ¿No prepara la tierra y la rompe para la semilla?
25 Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
Cuando se ha nivelado la faz de la tierra, ¿no pone las diferentes clases de semillas, y el grano en líneas, y la cebada y el centeno en los bordes?
26 Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
Porque su Dios es su maestro, que le da el conocimiento de estas cosas.
27 Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
Porque las piezas no se aplastan con un instrumento afilado, y una rueda de carro no se hace rodar sobre el comino; pero el grano de las hendiduras se martilla con un palo, y del comino con una varilla.
28 Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
¿Se tritura el grano para el pan? No lo sigue aplastando para siempre, pero deja que sus ruedas de carro y sus caballos lo pasen sin aplastarlo.
29 Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.
Esto viene del Señor de los ejércitos, haciendo maravillosos sus consejos y grande su sabiduría.