< Ishaya 28 >

1 Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
وای بر سامره! وای بر این شهری که با دره‌های حاصلخیز احاطه شده و مایۀ افتخار میگساران اسرائیل است! شراب، رهبران اسرائیل را از پای درآورده است. جلال اسرائیل که همانند تاج گلی بر سر رهبرانش بود، در حال پژمردن است.
2 Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
خداوند کسی را دارد که زورآور و توانا است. خداوند او را مانند تگرگ شدید و طوفان مهلک و سیلاب خروشان بر سرزمین اسرائیل می‌فرستد تا آن را فرا بگیرد.
3 Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
آنگاه شهری که مایهٔ افتخار میگساران اسرائیل است زیر پاها پایمال خواهد شد.
4 Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
شکوه و زیبایی دره‌های حاصلخیز آن ناگهان از بین خواهد رفت درست مانند نوبر انجیر که به محض دیده شدن بر سر شاخه‌ها، چیده و خورده می‌شود.
5 A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
روزی خواهد آمد که خداوند لشکرهای آسمان، خود برای بازماندگان قومش تاج جلال و زیبایی خواهد بود.
6 Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
او به قضات توانایی تشخیص خواهد بخشید و به سربازان قدرت خواهد داد تا از دروازه‌های شهر دفاع کنند.
7 Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
اما اینک اشخاص مست اورشلیم را اداره می‌کنند! حتی کاهنان و انبیا نیز مستند؛ شراب ایشان را چنان مست و گیج کرده که قادر نیستند پیامهای خدا را دریابند و آنها را به مردم رسانده، آنان را ارشاد کنند.
8 Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
سفره‌هایشان پر از استفراغ و کثافت است و هیچ جای پاکیزه‌ای دیده نمی‌شود.
9 “Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
آنها می‌گویند: «اشعیا به چه کسی تعلیم می‌دهد؟ چه کسی به تعلیم او احتیاج دارد؟ تعلیم او فقط برای بچه‌ها خوب است!
10 Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
او هر مطلبی را بارها برای ما تکرار می‌کند و کلمه به کلمه توضیح می‌دهد.»
11 To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
چون مردم به این تعلیم گوش نمی‌دهند، خدا قوم بیگانه‌ای را خواهد فرستاد تا به زبان بیگانه با قوم خود سخن بگوید!
12 waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
خدا به قوم خود فرموده بود: «اینجا جای استراحت است؛ پس خستگان استراحت کنند. اینجا مکان آرامی است.» اما ایشان نخواستند بشنوند.
13 Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
پس خداوند هر مطلبی را بارها برای ایشان تکرار خواهد کرد و آن را کلمه به کلمه توضیح خواهد داد. این قوم افتاده، خرد خواهند شد و در دام خواهند افتاد و سرانجام اسیر خواهند شد.
14 Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
پس ای حکمرانان اورشلیم که همه چیز را به باد مسخره می‌گیرید، به آنچه خداوند می‌فرماید توجه کنید.
15 Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol h7585)
شما با فخر می‌گویید: «با مرگ معامله کرده‌ایم و با دنیای مردگان قرارداد بسته‌ایم. اطمینان داریم که هرگاه مصیبتی رخ دهد هیچ گزندی به ما نخواهد رسید؛ زیرا با دروغ و فریب برای خود مخفیگاه ساخته‌ایم.» (Sheol h7585)
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
پس خداوند یهوه چنین می‌فرماید: «اینک من سنگ بنیادی در صهیون می‌نهم، سنگ گرانبها و آزموده شده. این یک سنگ زاویۀ مطمئنی است که می‌شود بر آن بنا کرد. هر که توکل کند ترسان و لرزان نخواهد شد.
17 Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
انصاف، ریسمان آن و عدالت، شاقول آن خواهد بود.» بارش تگرگ پناهگاه شما را که بر دروغ استوار است ویران خواهد کرد و سیل مخفیگاه شما را خواهد برد.
18 Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol h7585)
قراردادی که با مرگ و دنیای مردگان بسته‌اید باطل خواهد شد، بنابراین وقتی مصیبت بیاید شما را از پای درمی‌آورد. (Sheol h7585)
19 A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
مصیبت روز و شب به سراغتان خواهد آمد و شما را گرفتار خواهد کرد. هر بار که پیامی از خدا بشنوید وحشت سراپایتان را فرا خواهد گرفت.
20 wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
شما مانند کسی خواهید بود که می‌خواهد بخوابد اما بسترش کوتاهتر از آنست که بر آن دراز بکشد و لحافش تنگ‌تر از آنکه او را بپوشاند.
21 Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
خداوند با خشم و غضب خواهد آمد تا کارهای شگفت‌انگیز خود را به انجام رساند همان‌گونه که در کوه فراصیم و درهٔ جبعون این کار را کرد.
22 Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
پس، از تمسخر دست بردارید مبادا مجازات شما سنگینتر شود، زیرا خداوند، خداوند لشکرهای آسمان به من گفته که قصد دارد تمام زمین را نابود کند.
23 Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
به من گوش کنید! به سخنان من توجه کنید!
24 Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
آیا کشاورز تمام وقت خود را صرف شخم زدن زمین می‌کند و در آن هیچ بذری نمی‌کارد؟ آیا او فقط به آماده کردن خاک سرگرم است و بس؟
25 Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
البته او می‌داند که باید آن را آماده کند تا در آن تخم بکارد. می‌داند تخم گشنیز و زیره را کجا بپاشد و بذر گندم و جو و ذرت را کجا بکارد.
26 Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
او می‌داند چه کند زیرا خدایش به او یاد داده است.
27 Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
او هرگز برای کوبیدن گشنیز و زیره از خرمنکوب استفاده نمی‌کند، بلکه با چوب آنها را می‌کوبد.
28 Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
برای تهیهٔ آرد، او می‌داند چه مدت باید گندم را خرمنکوبی کند و چگونه چرخ ارابهٔ خود را بر آن بگرداند بدون اینکه اسبان ارابه، گندم را له کنند.
29 Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.
تمام این دانش از خداوند لشکرهای آسمان که رأی و حکمتش عجیب و عظیم است صادر می‌گردد.

< Ishaya 28 >