< Ishaya 28 >

1 Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
Maye kulowomqhele wamaluba, iqhono lezidakwa zako-Efrayimi, kuluba elibunayo, ubuhle obukhazimulayo, obubekwe ngaphezulu kwesigodi esivundileyo, kulelodolobho, iqhono lalabo asebelaliswe liwayini phansi!
2 Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
Khangelani, uThixo ulaye olamandla oqinileyo. Njengesiqhotho lomoya odilizayo, njengezulu lesiphepho lesihlambi esilamandla, uzakuphosa phansi ngamandla amakhulu.
3 Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
Umqhele lowo wamaluba, iqhono lezidakwa zako-Efrayimi kuzanyathelwa ngaphansi kwezinyawo.
4 Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
Leliyaluba elibunayo, ubuhle bakhe obukhazimulayo, kuhlanyelwe ngaphezu kwesigodi esivundileyo, lizakuba njengomkhiwa ovuthiweyo kungakavunwa okuthi khonokho nje omunye ewubona awukhe ngesandla awuginye.
5 A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
Ngalolosuku uThixo uSomandla uzakuba ngumqhele okhazimulayo, umqhele wamaluba omuhle kulabo abayizinsalela zabantu bakhe.
6 Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
Uzakuba ngumoya wokulunga kulowo owahlulelayo, umthombo wamandla kulabo ababuyisela impi emuva isisesangweni.
7 Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
Lalaba bayadiyazela ngenxa yewayini, babhadazele ngenxa yotshwala. Abaphristi labaphrofethi bayadiyazela ngenxa yotshwala, njalo baphambene ngenxa yewayini; bayabhadazela ngenxa yotshwala, bayadiyazela, lapho bebona imibono, bayakhininda lapho besenza izinqumo.
8 Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
Amatafula wonke agcwele amahlanzo njalo akulandawo engelamanyala.
9 “Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
“Ngubani lowo ozama ukumfundisa? Umbiko wakhe uwuchazela bani na? Abantwana abangasamunyi, kumbe abalunyuliweyo na?
10 Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
Ngoba kumi kanje: Yenza lokhu, yenza lokhuya, umthetho walokhu, umthetho walokhuya; ingcosana lapha, lengconsana laphayana.”
11 To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
Kungasenani, ngezindebe zabezizweni langolimi olungaziwayo, uNkulunkulu uzakhuluma lalababantu,
12 waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
atshoyo kubo wathi, “Le yindawo yokuphumula, abadiniweyo kabaphumule”; njalo, “Le yindawo yokucambalala,” kodwa kabalalelanga.
13 Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
Ngakho ilizwi likaThixo kubo lizakuba ngelithi: Yenza lokhu, yenza lokhuya, umthetho walokhu, umthetho walokhuya, ingcosana lapha, ingcosana laphaya, ukuze bahambe bawe nyovane, balimale, bathiywe, bathunjwe.
14 Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
Ngakho-ke zwanini ilizwi likaThixo lina bantu abaklolodayo, ababusa abantu laba eJerusalema.
15 Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol h7585)
Lizitshaya izifuba lisithi, “Senze isivumelwano lokufa, senza isivumelwano lethuna. Nxa isijeziso esikhulu sifika, kasiyikusithinta, ngoba senze amanga aba yisiphephelo sethu lenkohliso yaba yindawo yethu yokucatsha.” (Sheol h7585)
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
Ngakho lokhu yikho okutshiwo nguThixo woBukhosi: “Khangelani, ngibeka ilitshe eZiyoni, ilitshe elihloliweyo, ilitshe lengosi eliligugu; elesisekelo esiqinisekileyo, lowo othembayo akayikuphela amandla.
17 Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
Ngizakwenza okufaneleyo kube yintambo yokulinganisa, ukulunga kube yintambo yokuqondisa; isiqhotho sizakhukhula isiphephelo senu, amanga, lamanzi azagabhela indawo yenu yokucatsha.
18 Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol h7585)
Isivumelwano senu lokufa sizakwesulwa; isivumelwano senu lengcwaba kasiyikuma. Lapho isijeziso esikhulu sifika sizalilahla phansi. (Sheol h7585)
19 A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
Ngazozonke izikhathi esizafika ngazo sizalithatha; ukusa ngokusa, emini lebusuku, sizalikhukhula.” Ukulizwisisa ilizwi leli kuzaletha ukwesaba khona ngokwakho.
20 wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
Umbheda mfitshane kakhulu ukuba unabe kuwo, ingubo incane kakhulu ukuba ugoqelwe ngayo.
21 Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
UThixo uzavuka njengalokho akwenzayo entabeni iPherazimu; uzathukuthela njengaseSigodini seGibhiyoni, ukuba enze umsebenzi wakhe, umsebenzi oyisimanga, enze umsebenzi wakhe, umsebenzi ongaziwayo.
22 Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
Khathesi-ke yekelani ukukloloda kwenu funa amaketane elibotshwe ngawo alisinde kakhulu; iNkosi, uThixo uSomandla usengitshele ngesimiso sokutshabalalisa ilizwe lonke.
23 Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
Lalelani lizwe ilizwi lami; lalelani lizwe engikutshoyo.
24 Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
Lapho umlimi elima ukuba ahlanyele, ulima kokuphela na? Uqhubeka elima umhlabathi ewubhuqa kokuphela na?
25 Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
Nxa umhlabathi esewendlale kuhle, kahlanyeli ikharawayi ahlanyele lekhumini na? Kahlanyeli ingqoloyi endaweni yayo; ibhali ensimini yayo, lespelithi ensimini yaso na?
26 Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
UNkulunkulu wakhe uyamfundisa, amfundise indlela eqondileyo.
27 Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
Ikharawayi kayibhulwa ngesileyi; lenqola kayihanjiswa phezu kwekhumini, kodwa ikharawayi ibhulwa ngentonga, kuthi ikhumini ibhulwe ngombhulo.
28 Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
Amabele kumele acholwe ukuba kwenziwe isinkwa, ngakho umuntu kawabhuli kokuphela. Lanxa ehambisa inqola yakhe yokubhula phezu kwawo, amabhiza akhe kawawacholi.
29 Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.
Konke lokhu lakho kuvela kuThixo uSomandla omangalisayo ngokweluleka, njalo olenhlakanipho emangalisayo.

< Ishaya 28 >