< Ishaya 28 >
1 Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
A UWE ka lei hookiekie o na mea ona ma Eperaima, Ka pua mae wale o kona nani maikai, Ka mea ma ko poo o ka papu momona, O na mea i ona i ka waina!
2 Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
Aia hoi, ka mea ikaika, ka mea i hooikaikaia e ka Haku, Nana no e hoohiolo ia lakou ilalo i ka lepo me kona lima, E like me ka huahekili e haule ana, E like hoi me ka ino nui e make ai, A me ka wai kahe he nui e holo moku ana.
3 Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
Malalo o na wawae e hahiia'i Na lei hookiekie o na mea ona ma Eperaima.
4 Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
Ka pua mae wale o kona nani maikai, Ka mea ma ke poo o ka papu momona, E like auanei ia me ka hua mua o ke kau, O ka mea nana aku a ike ia mea, Moni koke no ia i ka loaa ana i kona lima.
5 A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
A hiki aku i kela la, E lilo no o Iehova i lei alii maikai, A i papale alii nani, no ka poe i koe o kona poe kanaka,
6 Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
A i uhane hooponopono maloko o ka poe hooponopono, A i ikaika hoi iloko o ka poe i hoohuli i ke kaua ana i ka pukapa.
7 Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
Ua kunewanewa lakou nei, no ka waina, Ua hikaka lakou no ka inu awaawa, Ua kunewanewa ke kahunapule, a me ke kaula no ka inu awaawa, Ua oki loa lakou i ka waina, Ua hikaka lakou no ka inu awaawa, Ua kunewanewa lakou ma ka hihio, Ua kulanalana ko lakou hooponopono ana.
8 Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
No ka mea, ua paapu na papaaina a pau i ka luai, I ka paumaele hoi, aohe wahi kaawale.
9 “Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
Ia wai la ia e ao mai ai i ka ike? E hoike mai oia i ka naauao ia wai? I ka poe anei i ukuhiia i ka waiu? I ka poe anei i auaia i ka u?
10 Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
No ka mea, he rula maluna o ka rula, He rula maluna o ka rula; He loina maluna o ka loina, He loina maluna o ka loina; He uuku ma keia wahi. He uuku ma kela wahi.
11 To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
He oiaio no me ka lehelehe namu a me ka olelo o ka malihini, E olelo mai ai oia i keia poe kanaka.
12 waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
Ia ia i olelo aku ai ia lakou, Eia ka maha e hoomaha oukou i ka poe maloeloe, Eia ka hooluolu; aole nae lakou i hoolohe.
13 Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
Nolaila i hiki ai ka olelo a Iehova ia lakou, He rula maluna o ka rula, He rula maluna o ka rula; He loina maluna o ka loina, He loina maluna o ka loina; He uuku ma keia wahi, He uuku ma kela wahi; I hele ai lakou a hina ihope, a lukuia, I hoopaheleia hoi, a paa.
14 Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
Nolaila, e hoolohe oukou i ka olelo a Iehova, e na kanaka hoowahawaha, Ka poe e noho alii ana maluna o keia poe kanaka ma Ierusalema.
15 Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol )
No ka mea, ua olelo oukou, Ua hana makou i berita me ka make, Ua hookuikahi makou me ko ka po; A hiki mai ka hahau ana a mahuahua, Aole ia e hiki mai io makou nei; No ia mea, ua hoolilo makou i ka wahahee i puuhonua no makou, Ua huna makou ia makou iho iloko o ka hoopunipuni. (Sheol )
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
No ia mea, peneia ka olelo ana mai a ka Haku, a Iehova, Aia hoi, ke hoonoho nei au ma Ziona, He pohaku, he pohaku i hoaoia, He pohaku kihi, ua maikai, He poliaku kumu i hoonoho paa ia: O ka mea i hilinai aku ia ia, aole ia e hee.
17 Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
E hoopai pololei aku au ma ke kaula, A e hooponopono aku au ma ka hoailona kupono; A na ka huahekili e hoopau aku i ka puuhonua wahahee, A e halanaia i ka wai, kahi e pee aku ai.
18 Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol )
E hoopauia auanei ko oukou berita me ka make, Aole e kupaa ka oukou kuikahi ana me ka po; I ka wa e hiki mai ai ka hahau ana a mahuahua, E hahiia oukou ilalo e ia. (Sheol )
19 A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
I ka wa e puka mai ai ia, e hoopaa mai no ia ia oukou; He oiaio no e hiki mai ia i kela kakahiaka i keia kakahiaka, A i ke ao no hoi a me ka po; A e lilo no ka lohe wale i mea e makau ai.
20 wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
No ka mea, ua pokole kahi moe, aole hiki ke hoomoe loa malaila; Ua ololi kahi kapa moe, aole hiki ke uhi ia ia iho.
21 Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
No ka mea, e like me ia ma ka mauna o Perazima, Pela no e ala mai ai o Iehova; E like me ia ma ke kahawai o Gibeona, Pela no ia e huhu mai ai, I hana'i oia i kana hana, i kana hana kupanaha hoi; I hoopaa hoi oia i kana hana, kana hana ano e.
22 Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
Ano hoi, mai hoowahawaha oukou, O hoopaa loa ia ko oukou mau kupee; No ka mea, ua lohe au i ka hoopau ana, i hooholoia, Na ka Haku na Iehova o na kaua, i ka aina a pau.
23 Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
E haliu mai oukou, a e hoolohe i ko'u leo, E haliu mai oukou, a e hoolohe i ka'u olelo ana.
24 Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
O ka mea hana me ka oopalau, E hana anei ia i na la a pau e kanu ai? E wawahi ana, a e kuikui ana ia i puupuu lepo o kona aina?
25 Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
A hana aku oia i ka lepo a maniania, Aole anei ia i lulu iho i ke kumino eleele, A kanu no hoi i ke kumino? A lulu i ka hua palaoa maikai, A me ka bale, a me ka palaoa eleele, Ma kona wahi iho?
26 Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
Ao mai no kona Akua ia ia ma ka hooponopono, A hoike mai no hoi ia ia.
27 Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
Aole i kuiia ke kumino eleele i ka mea kui, Aole i hookaaia ka mea kaa maluna o ke kumino; Aka, ua kuiia ke kumino eleele i ka laau, A me ke kumino hoi i ka laau kui.
28 Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
Kuiia no ka palaoa a wali, No ka mea, aole makemake ia i ka hahi loihi ana, Aole hoi e hookaa aku i ke kaa o kona kaa, Aole hoi e hahi aku na lio ona ia mea.
29 Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.
I puka mai no keia mai o Iehova o na kaua mai, Ka mea kupanaha ma ka noonoo ana, A nui loa no hoi kona ike.