< Ishaya 28 >

1 Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
Malheur à la couronne orgueilleuse des ivrognes d'Éphraïm, à la fleur fanée, son plus bel ornement, qui domine la vallée fertile des hommes vaincus par le vin!
2 Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
Voici, le Seigneur tient en réserve un homme fort et puissant, semblable à un orage de grêle, à un ouragan destructeur, à une trombe de grosses eaux qui débordent. Il la jette par terre de la main.
3 Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
Elle sera foulée aux pieds, la couronne superbe des ivrognes d'Éphraïm.
4 Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
Et il en sera de la fleur fanée, son plus bel ornement, qui domine la vallée fertile, comme des fruits hâtifs avant la récolte; on les voit, et sitôt qu'on les a dans la main, on les dévore.
5 A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
En ce jour-là, l'Éternel des armées sera une couronne éclatante et un diadème de gloire pour le reste de son peuple;
6 Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
Un esprit de jugement pour celui qui est assis sur le siège de la justice, et une force pour ceux qui repoussent l'ennemi aux portes.
7 Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
Mais ils chancellent, eux aussi, par le vin; ils sont troublés par la boisson forte; sacrificateurs et prophètes chancellent par la boisson forte, ils sont vaincus par le vin, et troublés par la boisson forte; ils chancellent en prophétisant, ils vacillent en rendant la justice.
8 Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
Toutes leurs tables sont pleines de vomissement et d'ordures; il n'y a plus de place!
9 “Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
“A qui veut-il enseigner la sagesse, et à qui faire entendre l'instruction? Est-ce à des enfants sevrés, arrachés à la mamelle?
10 Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
Car il donne loi sur loi, loi sur loi, règle sur règle, règle sur règle, un peu ici, un peu là. “
11 To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
Aussi c'est par des lèvres qui balbutient et par une langue étrangère qu'il parlera à ce peuple.
12 waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
Il leur avait dit: C'est ici le repos, que vous donniez du repos à celui qui est accablé, c'est ici le soulagement. Mais ils n'ont pas voulu écouter.
13 Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
Aussi la parole de l'Éternel sera pour eux loi sur loi, loi sur loi, règle sur règle, règle sur règle, un peu ici, un peu là; afin qu'en marchant ils tombent à la renverse, qu'ils soient brisés, qu'ils tombent dans le piège, et qu'ils soient pris.
14 Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
C'est pourquoi, écoutez la parole de l'Éternel, hommes moqueurs, qui dominez sur ce peuple de Jérusalem.
15 Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol h7585)
Car vous dites: Nous avons fait alliance avec la mort, et nous avons fait accord avec le Sépulcre; quand le fléau débordé passera, il ne nous atteindra point; car nous avons pris la tromperie pour refuge, et le mensonge pour asile. (Sheol h7585)
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
C'est pourquoi, ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Voici, j'ai posé en Sion une pierre, une pierre angulaire, éprouvée et précieuse, solidement posée; celui qui s'y appuiera ne s'enfuira point.
17 Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
Je prendrai le droit pour règle et la justice pour niveau; et la grêle emportera le refuge de tromperie, et les eaux inonderont l'asile de mensonge.
18 Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol h7585)
Votre alliance avec la mort sera abolie, et votre accord avec le Sépulcre ne tiendra point. Quand le fléau débordé passera, vous serez foulés par lui. (Sheol h7585)
19 A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
Sitôt qu'il passera, il vous saisira; car il passera matin après matin, de jour et de nuit, et la frayeur seule sera votre instruction.
20 wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
Car le lit sera trop court pour s'y étendre, et la couverture trop étroite, quand on voudra s'envelopper.
21 Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
Car l'Éternel se lèvera, comme à la montagne de Pératsim; il se courroucera, comme dans la vallée de Gabaon, pour faire son œuvre, son œuvre inconnue, et pour exécuter son travail, son travail inaccoutumé.
22 Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
Et maintenant ne faites pas les moqueurs, de peur que vos liens ne se resserrent; car j'ai entendu que la destruction est résolue par le Seigneur, l'Éternel des armées, contre toute la terre.
23 Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
Prêtez l'oreille, écoutez ma voix; soyez attentifs, écoutez ma parole!
24 Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
Le laboureur qui veut semer, laboure-t-il toujours? Est-il toujours à ouvrir et à herser son terrain?
25 Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
Quand il en a aplani la surface, n'y répand-il pas l'anet, n'y sème-t-il pas le cumin? Ne met-il pas le froment par rangées, l'orge à la place marquée, et l'épeautre sur les bords?
26 Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
Son Dieu lui enseigne la règle à suivre, et l'instruit.
27 Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
Car l'anet ne se foule pas avec le rouleau; on ne fait pas tourner sur le cumin la roue du chariot; mais on bat l'anet avec une verge, et le cumin avec un fléau.
28 Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
On bat le blé, mais on ne le foule pas sans fin, en y poussant la roue du chariot, et le pied des chevaux ne l'écrase pas.
29 Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.
Cela procède aussi de l'Éternel des armées, qui est admirable en conseil et magnifique en moyens.

< Ishaya 28 >