< Ishaya 28 >

1 Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
Malheur à la couronne de fierté, des ivrognes d'Ephraïm, la noblesse de la gloire duquel n'est qu'une fleur qui tombe; ceux qui sont sur le sommet de la grasse vallée sont étourdis de vin.
2 Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
Voici, le Seigneur [a en main] un fort et puissant homme, ressemblant à une tempête de grêle, à un tourbillon qui brise tout, à une tempête de grosses eaux débordées; il jettera [tout] par terre avec la main.
3 Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
La couronne de fierté et les ivrognes d'Ephraïm seront foulés aux pieds.
4 Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
Et la noblesse de sa gloire qui est sur le sommet de la grasse vallée ne sera qu'une fleur qui tombe; ils seront comme les fruits hâtifs avant l'Eté, lesquels incontinent que quelqu'un a vus, il les dévore dès qu'il les a dans sa main.
5 A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
En ce jour-là l'Eternel des armées sera pour couronne de noblesse, et pour diadème de gloire au résidu de son peuple.
6 Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
Et pour esprit de jugement à celui qui sera assis [sur le siège] de jugement; et pour force à ceux qui dans le combat feront retourner les [commis] jusques à la porte.
7 Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
Mais ceux-ci aussi se sont oubliés dans le vin, et se sont fourvoyés dans la cervoise; le Sacrificateur et le Prophète se sont oubliés dans la cervoise; ils ont été engloutis par le vin, ils se sont fourvoyés a cause de la cervoise; ils se sont oubliés dans la vision, ils ont bronché dans le jugement.
8 Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
Car toutes leurs tables ont été couvertes de ce qu'ils ont rendu et de leurs ordures; tellement qu'il n'y a plus de place.
9 “Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
A qui enseignerait-on la science, et à qui ferait-on entendre l'enseignement? [ils sont comme] ceux qu'on vient de sevrer, et de retirer de la mamelle.
10 Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
Car [il faut leur donner] commandement après commandement; commandement après commandement; ligne après ligne; ligne après ligne; un peu ici, un peu là.
11 To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
C'est pourquoi il parlera à ce peuple-ci avec un bégayement de lèvres, et une langue étrangère.
12 waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
Il lui avait dit; c'est ici le repos, que vous donniez du repos à celui qui est lassé, et c'est ici le soulagement; mais ils n'ont point voulu écouter.
13 Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
Ainsi la parole de l'Eternel leur sera commandement après commandement; commandement après commandement; ligne après ligne; ligne après ligne; un peu ici, un peu là; afin qu'ils aillent et tombent à la renverse, et qu'ils soient brisés; et afin qu'ils tombent dans le piége, et qu'ils soient pris.
14 Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
C'est pourquoi écoutez la parole de l'Eternel, vous hommes moqueurs, qui dominez sur ce peuple qui [est] à Jérusalem;
15 Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol h7585)
Car vous avez dit; nous avons fait accord avec la mort, et nous avons intelligence avec le sépulcre; quand le fléau débordé traversera, il ne viendra point sur nous, car nous avons mis le mensonge pour notre retraite, et nous nous sommes cachés sous la fausseté. (Sheol h7585)
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
C'est pourquoi ainsi a dit le Seigneur, l'Eternel; voici je mettrai pour fondement une pierre en Sion, une pierre éprouvée, [la pierre] de l'angle le plus précieux, pour être un fondement solide; celui qui croira ne se hâtera point.
17 Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
Et je mettrai le jugement à l'équerre, et la justice au niveau; et la grêle détruira la retraite du mensonge, et les eaux inonderont le lieu où l'on se retirait.
18 Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol h7585)
Et votre accord avec la mort sera aboli, et votre intelligence avec le sépulcre ne tiendra point; quand le fléau débordé traversera, vous en serez foulés. (Sheol h7585)
19 A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
Dès qu'il traversera il vous emportera; or il traversera tous les matins, de jour, et de nuit; et dès qu'on en entendra le bruit il n'y aura que remuement.
20 wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
Car le lit sera trop court, et on ne pourra pas s'y étendre; et la couverture trop étroite quand on se voudra envelopper.
21 Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
Parce que l'Eternel se lèvera comme en la montagne de Pératsim, et il sera ému comme dans la vallée de Gabaon, pour faire son œuvre, son œuvre extraordinaire, et pour faire son travail, son travail non accoutumé.
22 Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
Maintenant donc ne vous moquez [plus], de peur que vos liens ne soient renforcés, car j'ai entendu de par le Seigneur l'Eternel des armées une consomption, qui est même déterminée sur tout le pays.
23 Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
Prêtez l'oreille, et écoutez ma voix; soyez attentifs, et écoutez mon discours.
24 Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
Celui qui laboure pour semer, labourera-t-il tous les jours? ne cassera-t-il pas, et ne rompra-t-il pas les mottes de sa terre?
25 Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
Quand il en aura égalé le dessus, ne sèmera-t-il pas la vesce; ne répandra-t-il pas le cumin, ne mettra-t-il pas le froment au meilleur endroit, et l'orge en son lieu assigné, et l'épeautre en son quartier?
26 Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
Parce que son Dieu l'instruit et l'enseigne touchant ce qu'il faut faire.
27 Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
Car on ne foule pas la vesce avec la herse, et on ne tourne point la roue du chariot sur le cumin; mais on bat la vesce avec la verge, et le cumin avec le bâton.
28 Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
Le [blé dont on fait le] pain se menuise, car [le laboureur] ne saurait jamais le fouler entièrement, et quoiqu'il l'écrase avec la roue de son chariot, néanmoins il ne le menuisera pas avec ses chevaux.
29 Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.
Ceci aussi procède de l'Eternel des armées, qui est admirable en conseil, et magnifique en moyens.

< Ishaya 28 >