< Ishaya 28 >
1 Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
Woe to the crown of pride, of the drunkards of Ephraim, and to the fading flower of his glorious ornament, which is on the eminence of the fat valley of those who are struck down by wine!
2 Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
Behold, [it cometh] mighty and strong from the Lord, as a tempest of hail, a storm of destruction; as a tempest of mighty overflowing waters, will he cast it down to the earth with force.
3 Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
Under feet shall be trodden the crown of pride of the drunkards of Ephraim:
4 Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
And the fading flower of his glorious ornament, which is on the eminence of the fat valley, shall be as its early ripe fruit before the summer; which one, when he just seeth it, while it is scarcely in his hand, hastily devoureth.
5 A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
On that day will the Lord of hosts be for a crown of glory, and for a diadem of beauty, unto the residue of his people,
6 Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
And for a spirit of judgment to him that sitteth in judgment, and for strength to those that drive back the battle to the gate [of the enemy].
7 Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
But these also are now stumbling through wine, and reeling through strong drink: priest and prophet are stumbling through strong drink, they are overpowered with wine, they reel through strong drink; they stumble in [divine] vision, they are unsteady in giving judgment.
8 Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
For all tables are full of vomit of filthiness, there is no place [clean].
9 “Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
Whom shall he teach knowledge? and whom shall he give to understand doctrine? those that are weaned from the milk, those that are taken from the breasts.
10 Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
For precept must be upon precept, precept upon precept; line upon line, line upon line; here a little, and there a little.
11 To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
For [as] with stammering lips and a foreign tongue will he speak to this people;
12 waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
When he said unto them, This is the rest, cause ye the weary to rest; and this is the refreshing; but they would not hear.
13 Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
Therefore shall be unto them the word of the Lord, precept upon precept, precept upon precept; line upon line, line upon line; here a little, and there a little; in order that they may go, and stumble backward, and be broken, and snared, and caught.
14 Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
Therefore hear the word of the Lord, ye scornful men, who rule this people that is in Jerusalem.
15 Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol )
Because ye have said, “We have entered into a covenant with death, and with the nether world have we made an agreement; the overflowing scourge, when it passeth by, shall not come at us; for we have made lies our refuge, and under falsehood have we sought a hiding-place.” (Sheol )
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
Therefore thus hath said the Lord Eternal, Behold, I have laid in Zion as a foundation a stone, a tried stone, a costly corner-stone, well founded: he that believeth will not make haste.
17 Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
And I will make of justice a measuring line, and of righteousness a plummet: and the hail shall sweep off the refuge of lies, and the hiding-place against the waters shall these flood away.
18 Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol )
And your covenant with death shall be annulled, and your agreement with the nether world shall not have permanence; the overflowing scourge, when it passeth by—then shall ye be trodden down by it. (Sheol )
19 A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
As often as it passeth by shall it take you; for morning by morning shall it pass by, by day and by night; and the mere understanding of the report shall cause terror.
20 wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
For the bed shall be too short for [a man] to stretch himself out [on it]: and the covering too narrow to wrap himself in.
21 Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
For as on mount Perazim will the Lord rise up, as in the valley of Gib'on will he be wroth, that he may do his work, his singular work; and to accomplish his labor, his strange labor.
22 Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
And now be ye no longer scornful, lest your bonds be made strong; for as completed and fully decreed have I heard it from the Lord Eternal of hosts over all the earth.
23 Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
Give ye ear, and hear my voice; listen, and hear my speech.
24 Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
Doth the ploughman plough all the time to sow? doth he open and harrow his ground [continually]?
25 Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
Is it not so? that, when he hath made level its surface he scattereth fennel, and streweth about cumin, and planteth the wheat in rows, and barley on its assigned [place], and millet on its proper spot?
26 Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
For his God instructed him rightly, taught him [so to do].
27 Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
Truly not with a threshing instrument is fennel threshed, and a wagon-wheel is not turned about upon cumin; but fennel is beaten out with a staff, and cumin with a stick.
28 Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
Bread-corn is crushed; but not for ever doth [man] keep threshing it; and though he drive over it the wheel of his wagon and his horses, he will not [thereby] crush it.
29 Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.
This also cometh forth from the Lord of hosts; wonderful is he in counsel, and excellent in [his] wise deeds.