< Ishaya 28 >
1 Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
Woe to the crown of pride of the drunkards of Ephraim, and to the fading flower of his glorious beauty, which is on the head of the fat valley of those who are overcome with wine!
2 Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
Behold, the Lord has a mighty and strong one. As a tempest of hail, a destroying storm, as a tempest of mighty waters overflowing, he will cast down to the earth with the hand.
3 Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
The crown of pride of the drunkards of Ephraim shall be trodden under foot.
4 Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
And the fading flower of his glorious beauty, which is on the head of the fat valley, shall be as the first-ripe fig before the summer, which, when he who looks upon it sees, while it is yet in his hand, he eats it up.
5 A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
In that day Jehovah of hosts will become a crown of glory, and a diadem of beauty, to the residue of his people,
6 Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
and a spirit of justice to him who sits in judgment, and strength to those who turn back the battle at the gate.
7 Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
And even these reel with wine, and stagger with strong drink. The priest and the prophet reel with strong drink. They are swallowed up of wine. They stagger with strong drink; they err in vision; they stumble in judgment.
8 Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
For all tables are full of vomit, filthiness, no place clean.
9 “Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
Whom will he teach knowledge? And whom will he make to understand the message? Those who are weaned from the milk, and drawn from the breasts?
10 Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
For it is precept upon precept, precept upon precept, line upon line, line upon line, here a little, there a little.
11 To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
No, but by men of strange lips and with another tongue he will speak to this people,
12 waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
to whom he said, This is the rest. Give ye rest to him who is weary. And this is the refreshing. Yet they would not hear.
13 Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
Therefore the word of Jehovah shall be to them precept upon precept, precept upon precept, line upon line, line upon line, here a little, there a little, that they may go, and fall backward, and be broken, and snared, and taken.
14 Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
Therefore hear the word of Jehovah, ye scoffers, who rule this people that is in Jerusalem.
15 Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol )
Because ye have said, We have made a covenant with death, and we are at agreement with Sheol. When the overflowing scourge shall pass through it shall not come to us, for we have made lies our refuge, and we have hid ourselves under falsehood. (Sheol )
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
Therefore thus says the lord Jehovah, Behold, I lay in Zion for a foundation, a stone, a tried stone, a precious corner-stone, a sure foundation. He who believes in him shall, no, not be shamed.
17 Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
And I will make justice the line, and righteousness the plummet. And the hail shall sweep away the refuge of lies, and the waters shall overflow the hiding-place.
18 Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol )
And your covenant with death shall be annulled, and your agreement with Sheol shall not stand. When the overflowing scourge shall pass through, then ye shall be trodden down by it. (Sheol )
19 A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
As often as it passes though, it shall take you. For morning by morning it shall pass through, by day and by night. And it shall be nothing but terror to understand the report.
20 wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
For the bed is shorter than what a man can stretch himself on it, and the covering narrower than what he can wrap himself in it.
21 Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
For Jehovah will rise up as in mount Perazim. He will be angry as in the valley of Gibeon, that he may do his work, his strange work, and bring to pass his act, his strange act.
22 Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
Now therefore be ye not scoffers, lest your bonds be made strong. For I have heard a decree of destruction from the Lord, Jehovah of hosts, upon the whole earth.
23 Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
Give ye ear, and hear my voice, hearken, and hear my speech.
24 Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
Does he who plows to sow plow continually? Does he continually open and harrow his ground?
25 Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
When he has leveled the face of it, does he not cast abroad the chick-peas, and scatter the cummin, and put in the wheat in rows, and the barley in the appointed place, and the spelt in the border of it?
26 Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
For his God instructs him aright, and teaches him.
27 Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
For the chick-peas are not threshed with a sharp instrument, nor is a cart wheel turned about upon the cummin, but the chick-peas are beaten out with a staff, and the cummin with a rod.
28 Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
Bread grain is ground, for he will not be always threshing it. And though the wheel of his cart and his horses scatter it, he does not grind it.
29 Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.
This also comes forth from Jehovah of hosts, who is wonderful in counsel, and excellent in wisdom.