< Ishaya 28 >
1 Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
Mano kaka unune malit un osimbo mar jomer man Efraim, maber mare malich biro rumo ka maua maner, mopidhi ei holo momiyo mana kaka josunga malwokore gi kongʼo!
2 Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
Ne, Ruoth Nyasaye nigi ngʼato man kod loch gi teko. Mana kaka pe kod yamo maketho piny, e kaka obiro kelo koth machwe mabubni giteko matiek gik moko duto manie lowo.
3 Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
Osimbo ma jomer man Efraim sungorego ibiro nyono gi tielo.
4 Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
Berne malich norum mana ka maua maner, mopidhi ei holo momiyo, mi nochal ka olemb ngʼowu mokwongo chiek, ngʼato angʼata monene pone, kendo chame ka rikni morum chuth.
5 A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
E kindeno Jehova Nyasaye Maratego nobedi kaka osimbo mar duongʼ maber ne joge manok modongʼ.
6 Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
Enobed e chuny jangʼad bura mowinjore kendo enojiw jolwenjeu makedo, e dhorangeyeu obed gichir kendo olochi.
7 Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
To jogi bende kwangʼ nikech divai kendo gibayo nikech kongʼo: Jodolo kod jonabi mer makwangʼ nikech kongʼo kendo gitagore nikech divai, githembo ka gineno fweny, gichwanyore ka gingʼado bura.
8 Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
Mesa duto opongʼ gi ngʼok, onge kamoro amora ma ok dungʼ tik marach.
9 “Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
“En ngʼa motemo puonjo? To koso en ngʼa ma otemo yarone tiend wachne? Ne nyithindo mogolie chak, koso ne joma koro eka ogolie thuno?
10 Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
Onyisowa weche mak winjre ka mag jomomer ni: Tim ma, tim macha kendo tim ma, tim macha.”
11 To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
To kata kamano Nyasaye biro wuoyo gi jogi gi dho welo kod dhok mayoreyore.
12 waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
Mowachone niya, “Ma en kar yweyo, joma ool mondo oywe.” Kendo niya, “Ma en kar kwe,” to ne ok ginyal winjo.
13 Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
Kuom mano, wach Jehova Nyasaye biro chalonegi mana ka wach awacha mar joma omer niya: Tim ma, tim macha, kendo tim ma, tim macha, matin ka, matin kacha, mamiyo gikwangʼ koni gi koni mi gipodhi kendo gihinyre ma makgi e obadho.
14 Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
Kuom mano winjuru wach Jehova Nyasaye un joma jaro ji ma, jotend ogandani modak Jerusalem.
15 Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol )
Usungoru niya, “Wasetimo singruok gi tho wasedonjo e winjruok gi liete omiyo, ka masira miwachono nolandre e piny to ok nomulwa, nimar waseketo miriambo ragengʼ-wa, kendo wuondruok ka kar pondo.” (Sheol )
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
Ma e gima Jehova Nyasaye Manyalo Gik Moko Duto wacho, “Ne, aketo kidi e Sayun, ma en kidi moyier, en kidi motegno, ma nengone tek, moriwo kor ot kendo man-gi mise mongirore; ma ngʼat moyie kuome ok nobam.
17 Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
Abiro miyo adiera bedo tol mipimogo kendo tim makare kaka rapim mirieyogo ot; to kodh pe biro yweyo karu mar pondo, un jo-miriambo kendo pi biro pongʼo kuondeu mag tony.
18 Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol )
Singruok maru gi tho nobed maonge; kendo winjruok mane utimo gi liete ok nobedi. Ka masira nomwomre, to mano ema nochwadu piny. (Sheol )
19 A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
E kinde duto ma masira nobi enotieku; noyweu okinyi ka okinyi kendo odiechiengʼ gotieno.” Ka wachni nodonjne ji, to ginibed gi bwok maduongʼ.
20 wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
Kitanda nobed machiek ma ok nyal rieye tielo tir, kendo onget nobed matin ma ok nyal umo ngʼato maber.
21 Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
To Jehova Nyasaye biro aa malo mana kaka notimo e Got Perazim, mirimbe nowuogi kaka ne otimore e Holo mar Gibeon, mondo oti tichne, tichne mayoreyore ma ji kia kendo timne mar wich teko.
22 Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
Koro weuru ajara mondo kik tol motweugo ridre, nimar Ruoth Nyasaye ma en Jehova Nyasaye Maratego, osenyisa wach mar kethruok mabiro kwako piny duto.
23 Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
Chik iti kendo iwinj dwonda, keturu chunyu mondo uwinj weche mawacho.
24 Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
Ka japur puro puodho mondo okom to bende osiko ka opuro apura? Koso bende osiko ka obuso abusa?
25 Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
Kosetieko loso puothe donge ochwoyo kothe mopogore opogore kendo okiro kal? To donge opidho shairi kanyo kod ngano e bath puodho?
26 Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
Nyasache nyise yo monego oluw kendo puonje yo maber.
27 Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
Cham moko ok din gi twor to bende kal ok wuothie wiye gi gari; moko to idino gi luth kendo kal itengʼo gi kede.
28 Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
Ngano nyaka regi mondo olos makati; omiyo ok dine amingʼa. Kata obedo ni oywayo gache mar dino kuome, to faresene ok rege.
29 Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.
Magi duto bende oa kuom Jehova Nyasaye Maratego, ma jangʼad rieko mowinjore, kendo ma parone ber ahinya.