< Ishaya 27 >

1 A wannan rana, Ubangiji zai yi hukunci da takobi, takobinsa mai tsanani, mai ƙarfi da kuma mai muguwar ɓarna, zai hukunta dodon ruwa macijin nan da ya kanannaɗe, dodon ruwa macijin nan mai murɗewa; zai kashe dodon nan na teku.
در آن روز، خداوند با شمشیر بسیار تیز و برندهٔ خود، لِویاتان را که ماری تیزرو و پیچنده است به سزای اعمالش خواهد رساند و آن اژدها را که در دریاست خواهد کشت.
2 A wannan rana, “Ku rera game da gonar inabi mai ba da’ya’ya ku ce
در آن روز، خداوند دربارهٔ تاکستان پر بار خود خواهد گفت:
3 Ni, Ubangiji na lura da ita; na yi ta yin mata banruwa. Na yi tsaronta dare da rana don kada wani yă yi mata ɓarna.
«من یهوه، از این تاکستان مراقبت می‌نمایم و مرتب آن را آبیاری می‌کنم. روز و شب مواظب هستم تا کسی به آن آسیبی نرساند.
4 Ban yi fushi ba. Da a ce ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suke kalubalanta na mana! Zan fita in yi yaƙi da su; da na sa musu wuta duka.
دیگر بر تاکستان خود خشمگین نیستم. اگر ببینم خارها مزاحمش هستند، آنها را یکجا آتش خواهم زد، مگر اینکه دشمنان قوم من تسلیم شوند و از من تقاضای صلح کنند.»
5 Ko kuma bari su zo wurina don mafaka; bari su yi sulhu da ni, I, bari su yi sulhu da ni.”
6 A kwanaki masu zuwa Yaƙub zai yi saiwa, Isra’ila zai yi toho ya kuma yi fure ya cika dukan duniya da’ya’ya.
زمانی خواهد رسید که اسرائیل ریشه خواهد زد، غنچه و شکوفه خواهد آورد و دنیا را از میوه پر خواهد ساخت.
7 Ubangiji ya buge shi kamar yadda ya bugi waɗanda suka buge shi? An kashe shi kamar yadda aka kashe waɗanda suka kashe shi?
خداوند به اندازه‌ای که دشمنان قوم اسرائیل را تنبیه کرده است این قوم را تنبیه نکرده است.
8 Ta wurin yaƙi da zaman bauta ka hukunta shi, da tsananin tsawa kuma ka kore shi, kamar a ranar da iskar gabas ta hura.
او برای مجازات اسرائیل، آنها را از سرزمینشان به دیار دور تبعید کرد گویی باد شرقی وزید و آنان را با خود برد.
9 A ta haka fa, za a yi kafarar laifin Yaƙub, wannan kuma zai zama cikakken amfanin kau da zunubinsa. Sa’ad da ya niƙa duwatsun bagade suka zama kamar allin da aka farfashe kucu-kucu, har ba sauran ginshiƙan Ashera ko bagadan ƙona turare da za a bari a tsaye.
او این کار را کرد تا گناه قوم اسرائیل را کفاره کند؛ و این ثمرۀ کامل پاک شدن گناه آنها خواهد بود. وقتی او تمام سنگهای مذبح را همچون سنگ آهک تکه‌تکه کند، ستونهای اشیره و مذبحهای بخور دیگر برپا نخواهند ماند.
10 Birni mai katanga ya zama kufai, yasasshen mazauni, an yashe shi kamar hamada; a can’yan maruƙa suke kiwo, a can suke kwance; sun kakkaɓe rassanta ƙaf.
شهرهای مستحکم اسرائیل خالی از سکنه شده و مانند بیابان متروک گردیده‌اند. در آنجا گاوها می‌چرند و شاخ و برگ درختان را می‌خورند.
11 Sa’ad da rassanta suka bushe, sai su kakkarye su mata kuma su zo su yi itacen wuta da su. Gama mutane ne marar azanci; saboda haka Mahaliccinsu bai ji tausayinsu ba, Mahaliccinsu bai nuna musu jinƙai ba.
وقتی شاخه‌های درختان خشک می‌شوند، از درخت می‌افتند و زنها آنها را جمع کرده، در اجاق می‌سوزانند. این قوم فهم ندارد، پس صانع و خالق آنها بر آنها رحم و شفقت نخواهد کرد.
12 A wannan rana Ubangiji zai tankaɗe daga Yuferites mai gudu zuwa Rafin Masar, ku kuma, ya Isra’ilawa, za a tattara ku ɗaya-ɗaya.
اما زمانی خواهد رسید که خداوند مانند کسی که خوشه‌های گندم را دانه‌دانه برمی‌چیند و از پوستش جدا می‌کند، بنی‌اسرائیل را از رود فرات تا مرز مصر جمع خواهد کرد.
13 Kuma a wannan rana zai busa ƙaho mai kāra sosai. Waɗanda suke mutuwa a Assuriya da kuma waɗanda aka kai zaman bauta a Masar za su zo su kuma yi wa Ubangiji sujada a dutse mai tsarki a Urushalima.
در آن روز، شیپور بزرگ نواخته خواهد شد و بسیاری از قوم یهود که به آشور و مصر تبعید شده‌اند باز خواهند گشت و خداوند را در اورشلیم بر کوه مقدّسش پرستش خواهند کرد.

< Ishaya 27 >