< Ishaya 27 >

1 A wannan rana, Ubangiji zai yi hukunci da takobi, takobinsa mai tsanani, mai ƙarfi da kuma mai muguwar ɓarna, zai hukunta dodon ruwa macijin nan da ya kanannaɗe, dodon ruwa macijin nan mai murɗewa; zai kashe dodon nan na teku.
At that time, Yahweh will punish Leviathan, the swift-moving monster/dragon, that coiling serpent that lives in the sea. Yahweh will kill it with his sharp, huge, and powerful sword.
2 A wannan rana, “Ku rera game da gonar inabi mai ba da’ya’ya ku ce
At that time, [Yahweh will say], “You [Israeli people, who are like] [MET] a fruitful vineyard, must sing!
3 Ni, Ubangiji na lura da ita; na yi ta yin mata banruwa. Na yi tsaronta dare da rana don kada wani yă yi mata ɓarna.
I will [protect you] [like a farmer] [MET] waters his crops carefully [in order that they will grow well]. I will guard you day and night, in order that no one harms you.
4 Ban yi fushi ba. Da a ce ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suke kalubalanta na mana! Zan fita in yi yaƙi da su; da na sa musu wuta duka.
I am no [longer] angry [with my people]; [if any of your enemies try to injure you like briers and thorns injure people] [MET], I will attack them [in battles]; I will get rid of them completely,
5 Ko kuma bari su zo wurina don mafaka; bari su yi sulhu da ni, I, bari su yi sulhu da ni.”
unless they request me to protect them; I strongly invite them to make peace with me [DOU]!”
6 A kwanaki masu zuwa Yaƙub zai yi saiwa, Isra’ila zai yi toho ya kuma yi fure ya cika dukan duniya da’ya’ya.
There will be a time when the (descendants of Jacob/Israeli people) will [prosper like] a plant that has good roots; they will be like [MET] trees that bud and blossom and bear a lot of fruit; [what they do will bless] all the people in the world.
7 Ubangiji ya buge shi kamar yadda ya bugi waɗanda suka buge shi? An kashe shi kamar yadda aka kashe waɗanda suka kashe shi?
[But now I ask], has Yahweh punished us Israelis like he punished our enemies? Has he punished us as much as he punished them?
8 Ta wurin yaƙi da zaman bauta ka hukunta shi, da tsananin tsawa kuma ka kore shi, kamar a ranar da iskar gabas ta hura.
[No, he has not done that], [but] he punished us Israeli people and (exiled us/forced us to leave our country); we were taken away from our land as though [SIM] we were struck by a windstorm from the east.
9 A ta haka fa, za a yi kafarar laifin Yaƙub, wannan kuma zai zama cikakken amfanin kau da zunubinsa. Sa’ad da ya niƙa duwatsun bagade suka zama kamar allin da aka farfashe kucu-kucu, har ba sauran ginshiƙan Ashera ko bagadan ƙona turare da za a bari a tsaye.
Yahweh did that in order to punish us for our sins, and remove our guilt. As a result [of our being exiled], all the altars to other gods [in Israel] will be demolished, and we will be forgiven for the sins that we have committed. There will be no more poles for worshiping the goddess Asherah, or altars for burning incense to other gods; they will all be torn down.
10 Birni mai katanga ya zama kufai, yasasshen mazauni, an yashe shi kamar hamada; a can’yan maruƙa suke kiwo, a can suke kwance; sun kakkaɓe rassanta ƙaf.
The cities that have strong walls around them will be empty; like the desert, they will have no one living in them. The houses will be abandoned, and the streets will be full of weeds. Calves will eat grass there and lie down there; they will chew up all the leaves on the trees.
11 Sa’ad da rassanta suka bushe, sai su kakkarye su mata kuma su zo su yi itacen wuta da su. Gama mutane ne marar azanci; saboda haka Mahaliccinsu bai ji tausayinsu ba, Mahaliccinsu bai nuna musu jinƙai ba.
[The Israeli people are like] [MET] dry branches on a tree; women break them off and use them to make fires [under their cooking pots]. Our Israeli people do not have any sense; so Yahweh, who created them, will not act mercifully toward them or be kind to them.
12 A wannan rana Ubangiji zai tankaɗe daga Yuferites mai gudu zuwa Rafin Masar, ku kuma, ya Isra’ilawa, za a tattara ku ɗaya-ɗaya.
[However], there will be a time when Yahweh will gather them together [again; he will separate them from the people who have conquered them, like people] separate wheat from chaff. He will bring them [back to Israel], one by one, from [the land between] the Euphrates River [in the northeast] and the brook at the border of Egypt [in the southwest].
13 Kuma a wannan rana zai busa ƙaho mai kāra sosai. Waɗanda suke mutuwa a Assuriya da kuma waɗanda aka kai zaman bauta a Masar za su zo su kuma yi wa Ubangiji sujada a dutse mai tsarki a Urushalima.
At that time, a trumpet will be blown very loudly. And those who were exiled to Assyria and Egypt and who almost died there will return to Jerusalem, to worship Yahweh on [Zion], his holy hill.

< Ishaya 27 >