< Ishaya 27 >

1 A wannan rana, Ubangiji zai yi hukunci da takobi, takobinsa mai tsanani, mai ƙarfi da kuma mai muguwar ɓarna, zai hukunta dodon ruwa macijin nan da ya kanannaɗe, dodon ruwa macijin nan mai murɗewa; zai kashe dodon nan na teku.
In that day the LORD with his sore and great and strong sword shall punish leviathan the swift serpent, and leviathan the crooked serpent; and he shall slay the dragon that is in the sea.
2 A wannan rana, “Ku rera game da gonar inabi mai ba da’ya’ya ku ce
In that day: A vineyard of wine, sing ye unto it.
3 Ni, Ubangiji na lura da ita; na yi ta yin mata banruwa. Na yi tsaronta dare da rana don kada wani yă yi mata ɓarna.
I the LORD do keep it; I will water it every moment: lest any hurt it, I will keep it night and day.
4 Ban yi fushi ba. Da a ce ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suke kalubalanta na mana! Zan fita in yi yaƙi da su; da na sa musu wuta duka.
Fury is not in me: would that the briers and thorns were against me in battle! I would march upon them, I would burn them together.
5 Ko kuma bari su zo wurina don mafaka; bari su yi sulhu da ni, I, bari su yi sulhu da ni.”
Or else let him take hold of my strength, that he may make peace with me; [yea], let him make peace with me.
6 A kwanaki masu zuwa Yaƙub zai yi saiwa, Isra’ila zai yi toho ya kuma yi fure ya cika dukan duniya da’ya’ya.
In days to come shall Jacob take root; Israel shall blossom and bud: and they shall fill the face of the world with fruit.
7 Ubangiji ya buge shi kamar yadda ya bugi waɗanda suka buge shi? An kashe shi kamar yadda aka kashe waɗanda suka kashe shi?
Hath he smitten him as he smote those that smote him? or is he slain according to the slaughter of them that were slain by him?
8 Ta wurin yaƙi da zaman bauta ka hukunta shi, da tsananin tsawa kuma ka kore shi, kamar a ranar da iskar gabas ta hura.
In measure, when thou sendest her away, thou dost contend with her; he hath removed [her] with his rough blast in the day of the east wind.
9 A ta haka fa, za a yi kafarar laifin Yaƙub, wannan kuma zai zama cikakken amfanin kau da zunubinsa. Sa’ad da ya niƙa duwatsun bagade suka zama kamar allin da aka farfashe kucu-kucu, har ba sauran ginshiƙan Ashera ko bagadan ƙona turare da za a bari a tsaye.
Therefore by this shall the iniquity of Jacob be purged, and this is all the fruit of taking away his sin; when he maketh all the stones of the altar as chalkstones that are beaten in sunder, [so that] the Asherim and the sun-images shall rise no more.
10 Birni mai katanga ya zama kufai, yasasshen mazauni, an yashe shi kamar hamada; a can’yan maruƙa suke kiwo, a can suke kwance; sun kakkaɓe rassanta ƙaf.
For the defenced city is solitary, an habitation deserted and forsaken, like the wilderness: there shall the calf feed, and there shall he lie down, and consume the branches thereof.
11 Sa’ad da rassanta suka bushe, sai su kakkarye su mata kuma su zo su yi itacen wuta da su. Gama mutane ne marar azanci; saboda haka Mahaliccinsu bai ji tausayinsu ba, Mahaliccinsu bai nuna musu jinƙai ba.
When the boughs thereof are withered, they shall be broken off; the women shall come, and set them on fire: for it is a people of no understanding; therefore he that made them will not have compassion upon them, and he that formed them will shew them no favour.
12 A wannan rana Ubangiji zai tankaɗe daga Yuferites mai gudu zuwa Rafin Masar, ku kuma, ya Isra’ilawa, za a tattara ku ɗaya-ɗaya.
And it shall come to pass in that day, that the LORD shall beat off [his fruit], from the flood of the River unto the brook of Egypt, and ye shall be gathered one by one, O ye children of Israel.
13 Kuma a wannan rana zai busa ƙaho mai kāra sosai. Waɗanda suke mutuwa a Assuriya da kuma waɗanda aka kai zaman bauta a Masar za su zo su kuma yi wa Ubangiji sujada a dutse mai tsarki a Urushalima.
And it shall come to pass in that day, that a great trumpet shall be blown; and they shall come which were ready to perish in the land of Assyria, and they that were outcasts in the land of Egypt; and they shall worship the LORD in the holy mountain at Jerusalem.

< Ishaya 27 >