< Ishaya 27 >
1 A wannan rana, Ubangiji zai yi hukunci da takobi, takobinsa mai tsanani, mai ƙarfi da kuma mai muguwar ɓarna, zai hukunta dodon ruwa macijin nan da ya kanannaɗe, dodon ruwa macijin nan mai murɗewa; zai kashe dodon nan na teku.
On that day will the Lord punish with his heavy and great and strong sword leviathan the flying serpent, and leviathan the crooked servant; and he will slay the crocodile that is in the sea.
2 A wannan rana, “Ku rera game da gonar inabi mai ba da’ya’ya ku ce
On that day sing ye a song of the vineyard of excellent wine.
3 Ni, Ubangiji na lura da ita; na yi ta yin mata banruwa. Na yi tsaronta dare da rana don kada wani yă yi mata ɓarna.
“I the Lord do keep it; every moment will I water it: that no one shall hurt it, night and day will I keep it.
4 Ban yi fushi ba. Da a ce ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suke kalubalanta na mana! Zan fita in yi yaƙi da su; da na sa musu wuta duka.
Wrath have I not: who would set the briers and thorns against me in battle? I would pass through them, and I would burn them altogether.
5 Ko kuma bari su zo wurina don mafaka; bari su yi sulhu da ni, I, bari su yi sulhu da ni.”
If he but take hold of my strength, make peace with me; make peace with me.”
6 A kwanaki masu zuwa Yaƙub zai yi saiwa, Isra’ila zai yi toho ya kuma yi fure ya cika dukan duniya da’ya’ya.
In the future shall Jacob yet take root; Israel shall bud and blossom, and shall fill the face of the world with fruit.
7 Ubangiji ya buge shi kamar yadda ya bugi waɗanda suka buge shi? An kashe shi kamar yadda aka kashe waɗanda suka kashe shi?
Hath he smitten him, as he smote the one that smote him? or was he slain with the same slaughter as those of him that were slain?
8 Ta wurin yaƙi da zaman bauta ka hukunta shi, da tsananin tsawa kuma ka kore shi, kamar a ranar da iskar gabas ta hura.
In measure, by driving him forth, thou strivest with him: he removed him with his violent storm on the day of the east wind.
9 A ta haka fa, za a yi kafarar laifin Yaƙub, wannan kuma zai zama cikakken amfanin kau da zunubinsa. Sa’ad da ya niƙa duwatsun bagade suka zama kamar allin da aka farfashe kucu-kucu, har ba sauran ginshiƙan Ashera ko bagadan ƙona turare da za a bari a tsaye.
Therefore by this [only] shall the iniquity of Jacob be atoned; and this shall be all the fruit of the taking away of his sin; when he maketh all the stones of the altar as limestones that are beaten in pieces, when there shall not arise again any groves and sun-images.
10 Birni mai katanga ya zama kufai, yasasshen mazauni, an yashe shi kamar hamada; a can’yan maruƙa suke kiwo, a can suke kwance; sun kakkaɓe rassanta ƙaf.
For [by this] the fortified city shall be desolate, the habitation be forsaken, and left like a wilderness; there shall the calf feed, and there shall it lie down, and consume its branches.
11 Sa’ad da rassanta suka bushe, sai su kakkarye su mata kuma su zo su yi itacen wuta da su. Gama mutane ne marar azanci; saboda haka Mahaliccinsu bai ji tausayinsu ba, Mahaliccinsu bai nuna musu jinƙai ba.
When its boughs are withered, they shall be broken off; women will come and set them on fire; for it is not a people of understanding; therefore he that made it will not have mercy on it, and he that formed it will show it no favor.
12 A wannan rana Ubangiji zai tankaɗe daga Yuferites mai gudu zuwa Rafin Masar, ku kuma, ya Isra’ilawa, za a tattara ku ɗaya-ɗaya.
And it shall come to pass on that day, that the Lord will beat off [the fruit] from the channel of the River up to the brook of Egypt; but ye shall be gathered up one by one, ye children of Israel.
13 Kuma a wannan rana zai busa ƙaho mai kāra sosai. Waɗanda suke mutuwa a Assuriya da kuma waɗanda aka kai zaman bauta a Masar za su zo su kuma yi wa Ubangiji sujada a dutse mai tsarki a Urushalima.
And it shall come to pass on that day, that the great cornet shall be blown, and then shall come those who are lost in the land of Asshur, and those who are outcasts in the land of Egypt, and they shall prostrate themselves before the Lord on the holy mount at Jerusalem.