< Ishaya 27 >
1 A wannan rana, Ubangiji zai yi hukunci da takobi, takobinsa mai tsanani, mai ƙarfi da kuma mai muguwar ɓarna, zai hukunta dodon ruwa macijin nan da ya kanannaɗe, dodon ruwa macijin nan mai murɗewa; zai kashe dodon nan na teku.
到那日,耶和华必用他刚硬有力的大刀刑罚鳄鱼—就是那快行的蛇,刑罚鳄鱼—就是那曲行的蛇,并杀海中的大鱼。
2 A wannan rana, “Ku rera game da gonar inabi mai ba da’ya’ya ku ce
当那日,有出酒的葡萄园, 你们要指这园唱歌说:
3 Ni, Ubangiji na lura da ita; na yi ta yin mata banruwa. Na yi tsaronta dare da rana don kada wani yă yi mata ɓarna.
我—耶和华是看守葡萄园的; 我必时刻浇灌, 昼夜看守, 免得有人损害。
4 Ban yi fushi ba. Da a ce ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suke kalubalanta na mana! Zan fita in yi yaƙi da su; da na sa musu wuta duka.
我心中不存忿怒。 惟愿荆棘蒺藜与我交战, 我就勇往直前, 把它一同焚烧。
5 Ko kuma bari su zo wurina don mafaka; bari su yi sulhu da ni, I, bari su yi sulhu da ni.”
不然,让它持住我的能力, 使它与我和好, 愿它与我和好。
6 A kwanaki masu zuwa Yaƙub zai yi saiwa, Isra’ila zai yi toho ya kuma yi fure ya cika dukan duniya da’ya’ya.
将来雅各要扎根, 以色列要发芽开花; 他们的果实必充满世界。
7 Ubangiji ya buge shi kamar yadda ya bugi waɗanda suka buge shi? An kashe shi kamar yadda aka kashe waɗanda suka kashe shi?
主击打他们, 岂像击打那些击打他们的人吗? 他们被杀戮, 岂像被他们所杀戮的吗?
8 Ta wurin yaƙi da zaman bauta ka hukunta shi, da tsananin tsawa kuma ka kore shi, kamar a ranar da iskar gabas ta hura.
你打发他们去, 是相机宜与他们相争; 刮东风的日子, 就用暴风将他们逐去。
9 A ta haka fa, za a yi kafarar laifin Yaƙub, wannan kuma zai zama cikakken amfanin kau da zunubinsa. Sa’ad da ya niƙa duwatsun bagade suka zama kamar allin da aka farfashe kucu-kucu, har ba sauran ginshiƙan Ashera ko bagadan ƙona turare da za a bari a tsaye.
所以,雅各的罪孽得赦免, 他的罪过得除掉的果效,全在乎此: 就是他叫祭坛的石头变为打碎的灰石, 以致木偶和日像不再立起。
10 Birni mai katanga ya zama kufai, yasasshen mazauni, an yashe shi kamar hamada; a can’yan maruƙa suke kiwo, a can suke kwance; sun kakkaɓe rassanta ƙaf.
因为坚固城变为凄凉, 成了撇下离弃的居所,像旷野一样; 牛犊必在那里吃草, 在那里躺卧,并吃尽其中的树枝。
11 Sa’ad da rassanta suka bushe, sai su kakkarye su mata kuma su zo su yi itacen wuta da su. Gama mutane ne marar azanci; saboda haka Mahaliccinsu bai ji tausayinsu ba, Mahaliccinsu bai nuna musu jinƙai ba.
枝条枯干,必被折断; 妇女要来点火烧着。 因为这百姓蒙昧无知, 所以,创造他们的必不怜恤他们; 造成他们的也不施恩与他们。
12 A wannan rana Ubangiji zai tankaɗe daga Yuferites mai gudu zuwa Rafin Masar, ku kuma, ya Isra’ilawa, za a tattara ku ɗaya-ɗaya.
以色列人哪,到那日,耶和华必从大河,直到埃及小河,将你们一一地收集,如同人打树拾果一样。
13 Kuma a wannan rana zai busa ƙaho mai kāra sosai. Waɗanda suke mutuwa a Assuriya da kuma waɗanda aka kai zaman bauta a Masar za su zo su kuma yi wa Ubangiji sujada a dutse mai tsarki a Urushalima.
当那日,必大发角声,在亚述地将要灭亡的,并在埃及地被赶散的,都要来,他们就在耶路撒冷圣山上敬拜耶和华。